Sarki Sanusi ya bayyana ainahin abin da ke janyo rikicin addini a Najeriya

Sarki Sanusi ya bayyana ainahin abin da ke janyo rikicin addini a Najeriya

Mai martaba sarkin Kano, Muhammadu Sanusi Lamido II, ya bayyana cewa ba komai ke haddasa rikice-rikicen addini tsakanin Musulmi da Kirista ba a Najeriya illa rashin ilimi wato jahilci.

Sarki Sanusi wanda ya wakilci sarkin Musulmai kuma Sultan na Sokoto, Alhaji Abubakar Sa’ad a wani taro da ke gudana kan mafita ga rikice-rikicen addini a Najeriya a Abuja, ya ce a tarihi akwai lokacin da Musulmai suka taba zuwa hijira wajen Shugaban kiristoci a kasar habasha.

Mai martaba sarkin ya cigaba da cewa yadda ake watsa labaran karya a shafukan sadarwa na daga cikin abubuwan da ke bunkasa matsalar rikicin addini.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Zargin rashawa: Tsohon ministan shari’a, Mohammed Adoke ya isa kotu don gurfanar dashi

Shi ma a nasa jawabin, Rabaran Mathew Hassan Kuka ya ce ya yi kisan jama'ar da ake yi a Najeriya ya isa haka inda ya nemi da a hada hannu a tunkari gwamnati domin ta dakatar da hakan.

A wani labari na daban, mun ji cewa kungiyar gwamnonin Arewa ta yi Allah-wadai da kisan Reverend Lawan Andimi, wanda ya kasance Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) na gida kuma babban fasto a yankin Michika, jihar Adamawa wanda kungiyar yan ta’adda ta yi.

Gwamnonin arewa sun bayyana cewa sun yi bakin ciki matuka kan lamarin.

A wani jawabi a Jos a ranar Laraba, 22 ga watan Janairu, Shugaban kungiyar gwamnonin arewan kuma Gwamnan jihar Plateau, Simon Bako Lalong ya bayyana lamarin a matsayin wani abun bakin ciki na rashin imani daga kungiyar yan ta’addan wacce ta yi kaurin suna wajen sanya radadi a zukatan yan Najeriya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng