'Yan Najeriya sun fi son daukar hoto dani fiye da tambayar kudi a wurina - Dangote
- Aliko Dangote, hamshakin mai kudin Afirka ya ce in ya ci karo da 'yan Najeriya basu tambayar shi kudi sai dai hoton selfie
- Ya bayyana cewa ya kan tuka kan shi don ganin gari a duk kwanakin karshen mako a birnin Legas dake kudancin kasar nan
- Dangote ne mafi arziki na 95 a duniya kamar yadda Bloomberg Billionaires Index na 2019 ya bayyana
Aliko Dangote, hamshakin mai kudin Afirka ya ce in ya hadu da 'yan Najeriya, bukatarsu hoto kawai da shi a maimakon su tambaye shi kudi.
Dangote ya sanar da hakan ne a hirar da aka yi dashi a kan rayuwar shi, dukiyar shi da kuma shirin shi a nan gaba wacce David Rubeinstein a wani shirin gidan talabijin da shi David Rubeinstein ke yiwa mutane tambayoyi. Ya ce ya kan tuka kan shi ya zagaye birnin Legas da kan shi a ranakun karshen mako.
Kamar yadda jerin sunayen manyan masu kudin duniya na Bloomberg Billionaires Index ya nuna, Dangote ne mutum na 95 mafi kudi a duniya. Ya ce 'yan Najeriya kan bukaci su yi hoton selfie ne a maimakon tambayar shi kudi.
"Mutane ba su tambayata kudi idan na fito yawon shakatawata cikin ranakun mako amma su kan bukaci mu yi hoton selfie," in ji shi.
KU KARANTA: Tsautsayi ba a sa maka rana: Zakara ya kashe wani mutumi
A wannan tattaunawar ne ya bayyana cewa ana cigaba da gina matatar man fetur din shi wacce za ta kasance mafi girma a duniya kuma za ta dinga sarrafa ganga 650,000 na danyen mai a kullum. Za a kaddamar da matatar ne a watan Janairu na 2020.
Dangote dai shi ne shugaban kamfanonin Dangote Group wadanda suke kasuwancin man fetur, siminti da sauransu a Najeriya da wasu kasashen Afirka.
Yana da arzikin da ya kai dala biliyan 15 a duniya.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng