Jama’a na tserewa yayinda Boko Haram suka karbe hanyar Damaturu-Maiduguri
Jama’a da dama na tserewa daga gidajensu sakamakon hare-haren yan ta’addan Boko Haram a hanyar babban titin Maiduguri/Damaturu.
Hankula sun tashi a karshen mako sakamakon rashin tsaro a Auno da kewayenta a karamar hukumar Konduga a jihar Borno.
Yan ta’addan na ta addaban masu mota da kauyawan da ke wajen tsawon makonni duk da yawan tashoshin binciken sojoji.
Mazauna yankin sun koka cewa ana kashe mutane da dama sannan ana garkuwa da wasu da dama a kullun.
Wani jigon garin ya ce: “A maraicen nan, sama da mutane 1,000 sun tsere daga gidajensu a Auno, da dama sun koma Maiduguri a ranar Asabar. A yanzu haka da nake magana, manyan motoci na kwashe kayayyakin mutane. Na roke su cewa kada su bari garin ya tarwatse amma sun ki ji.
KU KARANTA KUMA: 'Yan bindiga sun yi awon gaba da mutane 5 a Zamfara, sun bayar da lambarsu ta waya
“Ya kamata shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kawo mana dauki; mun zabe shi don kawo karshen yakin, amma abun bakin ciki muna komawa baya ta yadda a kullun ake kai hare-hare a hanyar Maiduguri/Damaturu."
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng