Fusatattu matasa sun yiwa soja mugun duka kan kashe wani mai siyar da takalma a Kaduna

Fusatattu matasa sun yiwa soja mugun duka kan kashe wani mai siyar da takalma a Kaduna

- Hankula sun tashi yayinda wani soja ya soki wani mai siyar da takalma da wuka

- Lamarin dai ya afku ne a babbar kasuwar Sheikh Gumi a ranar Alhamis

- Hakan ya tunzura matasa a wajen inda suka ji ma sojan mummunan rauni

An shiga rudani a babbar kasuwar Sheikh Gumi a ranar Alhamis, 16 ga watan Janairu lokacin da wani soja ya soki wani mai siyar da takalma da wuka.

Hakan ya sa fusatattun matasa a kasuwar suka far masa inda suka ji masa mummunan rauni.

Shaidu da abun ya faru a idanunsu sun bayyana cewa sojan wanda ke sanye da kayan gida ya dauki matakin ne bayan wani sabani ya shiga tsakaninsa da mai siyar da takalmin.

Ba a san cikakken abunda ya haddasa musun nasu ba amma lamarin ya faru da misalin karfe 2:30 na rana a .

“Wani soja ne ya chaki mai siyar da takalma da wuka bayan wani musu sannan matasan da ke wajen auka far masa inda suka ji ma sojan mummunan rauni a kai kafin a cece shi,” in ji wani shaida wanda ya bayyana kansa a matsayin Salisu.

KU KARANTA KUMA: Masu garkuwa da mutane sun saki basaraken da suka sace a Kano

Da aka tuntubi kakakin yan sandan jihar, DSP Yakubu Sabo, ya yi alkawarin samo cikakken bayani tare da tuntubar majiyarmu ta Daily Trust.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng