Mun shirya ma zaben da za a sake a Kano - INEC

Mun shirya ma zaben da za a sake a Kano - INEC

Kwamishinan zaben jihar Kano, Farfesa Riskua Shehu, ya bayyana a ranar Talata, 14 ga watan Janairu cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zabe na gaskiya a zaben da za a sake a kananan hukumomi tara na jihar.

Ya ce wata kotun daukaka kara a Kaduna a zama mabanbanta da tayi, ta yi umurnin sake zabe a mazabun tarayya da na jiha wanda biyu suka kasance daga Kiru/Bebeji da Tudun Wada Doguwa tare da rumfunar zabe biyu a mazabar Kumbotso, rumfunar zabe hudu a sauran mazabun jiha na Bunkure, Maobi, Minjibir da kuma Rogo, wanda dukkanin jam’iyyun jihar za su shiga ciki.

A cewarsa, zaben da za a sake zai gudana ne a wuraren rijista 60 a fadin kananan hukumomin da lamarin ya shafa tare da masu zabe 41,400 da aka yiwa rijista a rumfuna 698, wuraren zabe 166, ina gaba daya ya zama wuraren zabe 864.

Ya ce ana saura kwanaki 11 za a gudanar da zaben, INEC za ta kasance da dukkanin kayayyaki a kananan hukumomin da lamarin ya shafa, kamar yadda aka fara kai kayayyakin yayinda hukumar ke jiran isowar kayayyakin zabe daga hedkwatar, cewa za a sanar da dukkanin jam’iyyun siyasa da zarar CBN ta karbe su.

Ya ci gaba da bayanin cewa “Za a aika sakon gayyata ga wakilan dukkanin jam’iyyun siyasa da za su kasance a zaben da za a sake da kuma hukumomin tsaro don ganin yadda za a yi rabon kayayyakin."

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Buhari ya nada tsohon Shugaban DSS a matsayin Shugaban NISS

Yayinda ya ke martani kan shirye-shiryen zaben, ya ce ma’aikatan zabe na wucin gadi 3,456 za a dauka inda ya ce babu dan bautar kasar da za a tura Bebeji domin aiki a matsayin ma’aikacin wucin gadi saboda shawarar tsaro.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng