Yanzu Yanzu: Buhari ya nada tsohon Shugaban DSS a matsayin Shugaban NISS

Yanzu Yanzu: Buhari ya nada tsohon Shugaban DSS a matsayin Shugaban NISS

- Shugaba Muhammadu Buhari ya nada tsohon Darakta Janar ba hukumar tsaro na farin kaya (DSS), A.A. Gadzama, a matsayin Shugaban makarantar tsaro na kasa (NISS)

- Nadin wanda ya fara aiki daga ranar 16 ga watan Disamba 2019 zai shafe tsawon shekaru hudu

- Hakan na kunshe ne a wani jawabi daga babban sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada tsohon Darakta Janar ba hukumar tsaro na farin kaya (DSS), A.A. Gadzama, a matsayin Shugaban makarantar tsaro na kasa wato National Institute for Security Studies (NISS).

Nadin wanda ya fara aiki daga ranar 16 ga watan Disamba 2019 na kunshe ne a wani jawabi daga babban sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha.

Nadin zai shafe tsawon shekaru hudu ne.

A wani labarin kuma, Legit.ng ta rahoto a baya cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da kafa wasu kwamitoci guda biyu da zasu sanya idanu wajen gudanar da aikin samar da wutar Mamabilla na Megawatta 3050 a jahar Taraba, yankin Arewa ta tsakiya.

KU KARANTA KUMA: Gobara ta tashi a tsohuwar kasuwa a Sokoto

Kwamitocin guda biyu sun hada da kwamitin ministoci da zasu dinga tattaunawa tare da auna matsayin aikin a karkashin jagorancin ministan wutar lantarki, da kuma kwamitin tabbatar da an gudanar da aikin yadda ya kamata tare da kammala shi a lokacin daya dace.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng