Gwamnonin Jihohin Najeriya da aka yi a 1999 da Ubangiji ya dauki ransu

Gwamnonin Jihohin Najeriya da aka yi a 1999 da Ubangiji ya dauki ransu

A wannan karo kuma mun kawo maku jerin wasu tsofaffin gwamnoni ne da aka yi a Najeriya wanda yanzu sun riga mu gidan gaskiya.

Mun tattaro jerin gwamnonin bayan ne tare da takaitawa zuwa ga wadanda su ka yi mulki bayan sake shigowar mulkin farar hula a 1999.

1. Umaru ‘Yaradua

Marigayi Ummaru Musa ‘Yaradua ya bar Duniya ne shekaru 3 bayan ya sauka daga kujerar gwamnan Katsina, har ya zama shugaban kasa. ‘Yaradua ya rasu ne ya na kan mulkin kasa a 2010.

2. DSP Alamieyeseigha

Wannan tsohon gwamna da yanzu aka rasa a Najeriya shi ne Diepreye Solomon Peter Alamieyeseigha wanda ya yi gwamna a Bayelsa. Hawan jini ne ya kashe tsohon gwamnan a 2015.

3. Habubakar Habu Hashidu

Jama’a da dama sun manta da gwamnan jihar Gombe na farko na farar hula watau Abubakar Habu Hashidu. Alhaji Habu Hashidu ya rasu ne a tsakiyar 2018 bayan ya yi fama da rashin lafiya.

KU KARANTA: Gwamnonin da su ka fi shahara a shekarar bara a Najeriya

4. Muhammad Alabi Lawal

Tsohon gwamna Mohamamed Lawal shi ne ya fara riga mu gidan gaskiya daga cikin gwamnonin da su ka hau mulki a 1999. Lawal ya cika ne Nuwamban 2006 bayan wata rashin lafiya a Landan.

5. Abdulkadir Kure

Injiniya Abdulqadir Kure ya na daga cikin tsofaffin gwamnonin da yanzu aka rasa a Najeriya. Kure ya yi gwamna a Neja, sannan Ubangiji ya karbi ransa a kasar waje a farkon shekarar 2017.

6. Abubakar Mala Kachalla

Mala Kachalla wanda ya yi gwamna a jihar Borno daga 1999 zuwa 2003 a karkashin ANPP ya rasu ne a 2007. Kachalla ya sha kasa bayan da ya sauya-sheka ya nemi tazarce a zaben 2003.

7. Prince Abubakar Audu

Marigayi Abubakar Audu ya na cikin wadanda ba za a taba manta yadda mutuwa ta mamayesa ba. Audu ya gamu da mutuwar fuju’a ne yayin da ya ke daf da sake zama gwamnan Kogi a 2015.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Musulunci sai a bibiyi wannan shafi

https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel