Yanzu Yanzu: Allah ya yiwa Alkalin tarayya, Justis Ibrahim Maikaita Bako rasuwa

Yanzu Yanzu: Allah ya yiwa Alkalin tarayya, Justis Ibrahim Maikaita Bako rasuwa

Wani alkalin kotun tarayya, Justis Ibrahim Maikaita Bako, ya rasu a safiyar ranar Lahadi, 12 ga watan Janairu a wani asibitin Abuja sakamakon raunuka da ya ji a wani hatsarin mota da ya ritsa dashi a makon da ya gabata.

A tuna cewa hatsarin mota ya cika da alkalin a hanyar Funtua-Kankara da ke jihar Katsina a ranar 4 ga watan Janairu.

Majiyarmu ta Daily Trust ta ruwaito cewa an dauki Justis Bako wanda ya ji mummunan rauni zuwa Abuja domin samun kulawar likitoci inda ya mutu a safiyar yau Lahadi a asibitin Cedar Crest, Abuja.

Da yake tabbatar da mutuwar, babban alkalin jihar Katsina, Justis Musa Danladi ya ce: “Marigayi Bako ya rasu da misalin karfe 6:00 na safe a Cedar Crest, Abuja biyo bayan wani hatsarin mota a ranar Juma’a, makon da ya gabata inda ya ji mukmunan raunuka a baya da wuya.”

Ya Kara da cewa “ya kasance a sashin kulawa ta ICU inda likitoci suka yi kokari daidaita shi kafin a fita dashi kasar waje don magani.

KU KARANTA KUMA: Giwa ta fadi: Wani tsohon gwamna na kwance da shanyewar barin jiki, yana neman kudin magani

“An kuma yanke shawarar yin jana’izarsa tare da binne shi a Abuja bayan sallar Azahar. Wannan rashi ne babba.”

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng