Buhari ya bayar da umurnin gina gidaje 10,000 a jihar Borno

Buhari ya bayar da umurnin gina gidaje 10,000 a jihar Borno

- Shugaba Muhammadu Buhari ya dauki kwakwarar mataki don rage radadin wahalar da mutanen da ke sansanin 'yan gudun hijira suke ciki a Borno

- Shugaban kasar a ranar Juma'a 10 ga watan Janairu, ya bayar da umurnin gina gidaje 10,000 a jihar Borno

- Baya ga haka, Gwamna Babagana Umaru Zulum ya ziyarci sansanin 'yan gudun hijirar inda ya taimaka wurin raba musu bargo da sauran kayan sanyi da zai taimaka musu a wannan yanayin na hunturu

Shugaba Muhammadu Buhari ya bayar da kwangilar gina gidaje 10,000 a jihar Borno a cikin yunkurin da gwamnatin tarayya ke yi na farfado da jihar bayan barnar da ta'addancin Boko Haram ya yi.

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umaru Zulum ne ya bayyana hakan a ranar Juma'a 10 ga watan Janairu a shafinsa na Twitter.

Shugaban kasar ya yi wannan umurnin ne bayan Zulum ya ziyarci sansanin 'yan gudun hijira a ranar Alhamis, 9 ga watan Janairu inda ya kwana a can yana taimakawa wurin rabon kayan tallafi ga kimanin iyalai 1675.

DUBA WANNAN: Tashin hankali: Yadda wani mutum ya yi ta lalata da karya daga bisani ya kashe ta

Gwamnan ya kuma yi rabon barguna da daduma ga 'yan yi wa kasa hidima a jihar don taimaka musu magance sanyi a wannan yanayin na hunturu.

Ya kuma tabbatarwa 'yan gudun hijirar cewa yana nan kan bakansa na kokarin ganin an mayar da su garuruwansu idan an gama gine-gine.

Kazalika, Zulum ya yi wa 'yan gudun hijiran alkawarin cewa gwamnatin tarayya na iya kokarin ta don ganin ta kawoi karshen ta'addanci a jihar da sauran sassan kasar.

Gwamnan jihar na Borno ya kuma yabawa rundunar sojojin Najeriya kan matakin da ta dauka na gudanar da bincike kan zargin karbar kudade a hannun matafiya da ake ce sojoji na yi.

Legit.ng ta gano cewa Zulum ya yi wannan jawabin ne a daren Litinin 6 ga watan Janairu bayan mai kula da fanin yada labarai na soji, Aminu Iliyasu ya fitar da sanarwa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164