Sai dana sha kukana na more lokacin da aka biya ni albashina na farko a kasar Saudiyya - Likita dan Najeriya

Sai dana sha kukana na more lokacin da aka biya ni albashina na farko a kasar Saudiyya - Likita dan Najeriya

- Wani likitan Najeriya da ya koma kasar Saudi Arabia ya bayyana yadda ya fashe da kuka bayan da ya karba albashin shi na farko

- Ya ce a Najeriya yana duba marasa lafiya a kalla 100 zuwa 120 a rana amma ana biyanshi N118,000

- Amma albashin shi na farko a kasar waje an bashi $4,500 a watan farko da yayi a kasar Saudi Arabia

Wani likitan Najeriya da ya koma kasar Saudi Arabia ya bayyana yadda ya fashe da kuka bayan da ya karba jimillar albashinshi na watanni hudu Najeriya a kasar dake tsakiyar gabas din.

Bayan barin aikinshi a Najeriya, likitan ya wallafa yadda ya gane tsananin aikin tikin da yayi a kafar sada zumuntar zamani ta tuwita.

Ma’abocin amfani da kafar sada zumuntar ta tuwita kuma likitan, ya ce yana karbar N118,000 a matsayin albashinshi na wata daya a Najeriya. Hakazalika, yana duba marasa lafiya daga 100 zuwa 120 a kowacce rana.

Amma kuma bayan 2014 da ya koma kasar Saudi Arabia, an biya shi $4,500 na ganin a kalla marasa lafiya biyar zuwa bakwai a rana.

KU KARANTA: Garin dadi na nesa: Mutum 1 ne kacal ya mutu a birnin Oslo sanadiyyar hadarin mota a shekarar 2019 baki daya

Ga abinda ya wallafa: “A shekarar 2013 a Najeriya, ina aiyuka biyu ne. Safe da dare kuma ina ganin marasa lafiya a kalla 100 zuwa 120 a matsayina na likita. A karshen wata ina karbar N118,000.”

Ya kara da cewa:”Bayan da na gana intabiyu a kasar Saudi Arabia, sai aka tambayeni nawa za a dinga biya. Mamaki kuwa ya kama ni tun daga nan. A karshen wata kuwa sai aka biya ni $4,500. Jimillar albashi na kenan na watanni hudu. Ina duba marasa lafiya biyar zuwa bakwai a rana daya.”

Likitan ya kara da cewa fashewa yayi da kuka yayin da ya samu wannan albashi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel