Sai dana sha kukana na more lokacin da aka biya ni albashina na farko a kasar Saudiyya - Likita dan Najeriya

Sai dana sha kukana na more lokacin da aka biya ni albashina na farko a kasar Saudiyya - Likita dan Najeriya

- Wani likitan Najeriya da ya koma kasar Saudi Arabia ya bayyana yadda ya fashe da kuka bayan da ya karba albashin shi na farko

- Ya ce a Najeriya yana duba marasa lafiya a kalla 100 zuwa 120 a rana amma ana biyanshi N118,000

- Amma albashin shi na farko a kasar waje an bashi $4,500 a watan farko da yayi a kasar Saudi Arabia

Wani likitan Najeriya da ya koma kasar Saudi Arabia ya bayyana yadda ya fashe da kuka bayan da ya karba jimillar albashinshi na watanni hudu Najeriya a kasar dake tsakiyar gabas din.

Bayan barin aikinshi a Najeriya, likitan ya wallafa yadda ya gane tsananin aikin tikin da yayi a kafar sada zumuntar zamani ta tuwita.

Ma’abocin amfani da kafar sada zumuntar ta tuwita kuma likitan, ya ce yana karbar N118,000 a matsayin albashinshi na wata daya a Najeriya. Hakazalika, yana duba marasa lafiya daga 100 zuwa 120 a kowacce rana.

Amma kuma bayan 2014 da ya koma kasar Saudi Arabia, an biya shi $4,500 na ganin a kalla marasa lafiya biyar zuwa bakwai a rana.

KU KARANTA: Garin dadi na nesa: Mutum 1 ne kacal ya mutu a birnin Oslo sanadiyyar hadarin mota a shekarar 2019 baki daya

Ga abinda ya wallafa: “A shekarar 2013 a Najeriya, ina aiyuka biyu ne. Safe da dare kuma ina ganin marasa lafiya a kalla 100 zuwa 120 a matsayina na likita. A karshen wata ina karbar N118,000.”

Ya kara da cewa:”Bayan da na gana intabiyu a kasar Saudi Arabia, sai aka tambayeni nawa za a dinga biya. Mamaki kuwa ya kama ni tun daga nan. A karshen wata kuwa sai aka biya ni $4,500. Jimillar albashi na kenan na watanni hudu. Ina duba marasa lafiya biyar zuwa bakwai a rana daya.”

Likitan ya kara da cewa fashewa yayi da kuka yayin da ya samu wannan albashi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng