Isa Zarewa: Tsohon sanata daga jihar Kano ya mutu a Abuja

Isa Zarewa: Tsohon sanata daga jihar Kano ya mutu a Abuja

Allah ya yiwa tsohon sanatan Najeriya daga jihar Kano, Isa Yahaya Zarewa, rasuwa a daren ranar Litinin a Abuja.

Tsohon Sanatan ya rasu ne da misalin karfe 2:15 na daren ranar Litinin dare a gidansa dake Babban birnin tarayya, Abuja.

Majiyar Legit.ng ta sanar da ita cewa sanata Zarewa ya fara jin alamun rashin lafiya yayin da yake sauraron wa'azi a wani Masallaci da ke Abuja.

A cewar majiyar, tsohon Sanatan ya kira direbansa tare da umartarsa a kan ya kai shi ofishinsa daga Masallacin, kafin daga bisani ya umarce shi ya kai shi asibiti daga ofishin nasa.

Duk da ba bayyana lokacin da za a yi masa sallar Jana'iza ba a cikin sanarwar da Legit.ng ta samu, sanarwar ta bayyana cewa jirgin sama zai dauki gawar Sanata zarewa zuwa gidansa da ke unguwar Yahaya Gusau a cikin birnin Kano, inda za a yi masa sutura.

DUBA WANNAN: Fallasa: An gano yadda Abba Kyari ya ingiza Buhari ya kwace jagorancin kwamitin NLTP daga hannun Osinbajo

Majiyar mu ta tabbatar da cewa ta samu labarin mutuwar tsohon Sanatan ne daga Babban hadiminsa a kafar sada zumunta (Social media) Musa Shehu Musa.

An haifi tsohon Sanata Isa Zarewa a garin Zarewa da ke karkashin karamar hukumar Rogo ta jihar Kano a shekarar 1958, kuma ya wakilci jihar Kano ta kudu a majalisar dattijai daga shekarar 1999 zuwa 2003 a karkashin inuwar jam'iyyar PDP.

Sanata Zarewa ya yi gwagwarmayar siyasa a jam'iyyu da dama da suka hada da SDP, PDP, APC da jam'iyyar PRP, wacce ya koma bayan ya rasa tikitin takarar Sanata a jam'iyyar APC a zaben fidda 'yan takara a shekarar 2018.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel