Tikashi! Kwarto ya ziyarci dakunan kwanan dalibai mata a jami’ar ABU (bidiyo)

Tikashi! Kwarto ya ziyarci dakunan kwanan dalibai mata a jami’ar ABU (bidiyo)

Idan da ranka ka sha kallo, koda dai ba sabon abu bane kama kwartaye a lokacin da suke shirin shiga dakunan kwanan dalibai mata, musamman a jami’o’i.

Hakan ce ta kasance bisa ga wani labari mai ban al’ajabi da muka samu na kama wani tsoho a lokacin da yake yunkurin shiga dakin kwanan dalibai mata.

A bisa ga wani shafin mai suna northern_hibiscuss, daya daga cikin daliban makarantar wacce ta kasance mabiya shafin ce ta turo da labarin hade da bidiyon lamarin.

Ta ce an kama tsohon ne a dakin kwanan dalibai na Ribado hall, ABU Samaru, Zaria, da misalin karfe 4:00 na tsakar dare.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Gwamnoni na ganawa a Abuja

Ga yadda ta wallafa a shafin nata: "Salam Malama! Yau kawai Saiga tsohon banza a hostel dinmu(Ribado hall, ABU Samaru, Zaria.) wlh da daddare sbd karfe hudu(04:00) batayiba aka kamashi...kuma wlh abinda ya bani haushi securities a gal's hostel wulakanta mutane sukeyi akan ID card kokai student ne bazasu barshi ya shiga ba amma saiga namiji alama ma a nan ya Kwana..."

Ga yadda rubutun ya zo tare da bidiyon a kasa:

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng