Hotuna: 'Yar shekara biyar ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu a jihar Zamfara

Hotuna: 'Yar shekara biyar ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu a jihar Zamfara

- Wata yarinya a jihar Zamfara ta shiga tarihin gwamnonin jihar yayin da ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu kacal

- Gwamnan ya bata wannan dama ne saboda irin kokarin da take da shi a fannin ilimin zamani da kuma na addini

- Yarinyar ta sanya hannu akan wasu manyan dokoki na jihar da suka hada da fannin tsaro da kuma cigaban jihar ta Zamfara

Wata yarinya 'yar shekara biyar a duniya ta zama gwamnar jihar Zamfara ta rikon kwarya ta tsawon minti biyu.

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Muhammad Matawalle ya mika ragamar mulkin jihar Zamfaran na tsawon mintuna biyu ga wata karamar yarinya 'yar asalin karamar hukumar Tsafe dake jihar ta Zamfara.

Hotuna: 'Yar shekara biyar ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu a jihar Zamfara
Asma'u Habibu
Asali: Facebook

Yarinyar mai suna Asma'u Habibu Tsafe 'yar makarantar firamare ce ta Ali Akilu Model School dake garin na Tsafe.

Gwamna Bello Muhammad Matawalle ya bayar da ragamar mulkin jihar na tsawon mintuna biyu ga yarinyar ne saboda kwazon ta a fannin ilimin boko da na addini.

Hotuna: 'Yar shekara biyar ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu a jihar Zamfara
Asma'u Habibu
Asali: Facebook

KU KARANTA: Sojoji sun ceto daliban sakandare da aka yi garkuwa da su a Kaduna

Gwamnan rikon kwaryar ta rattaba hannu tare da zartar da wasu manyan ayyuka a jihar da suka shafi fannin tsaro da ci gaban jihar ta Zamfara.

An dai hasko hotunan yarinyar a lokacin da take zaune akan kujerar gwamnan jihar ta Zamfara rike da abin rubutu ga tulin takardu nan a gabanta, yayin da a gefe daya kuma aka nuno taron mutane da suka hada da 'yan fadar gwamnan jihar da kuma 'yan jarida.

Hotuna: 'Yar shekara biyar ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu a jihar Zamfara
Asma'u Habibu
Asali: Facebook

Hotuna: 'Yar shekara biyar ta zama gwamnan rikon kwarya ta minti biyu a jihar Zamfara
Asma'u Habibu
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel