Gwamna Zulum ya bawa matashin da ya lashe gasar Alqur'ani kyautar N5m, sabuwar mota da sauransu

Gwamna Zulum ya bawa matashin da ya lashe gasar Alqur'ani kyautar N5m, sabuwar mota da sauransu

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bawa matashin nan, Idris Abukakar Muhammad, kyautar makudan kudi, miliyan N5, tare da gaureriyar sabuwar mota kirar Toyota Corolla biyo bayan nasarar da ya samu a gasar musabaqar Alqur'ani ta kasa da kasa.

Bayan kyautar kudi da mota, gwamna Zulum ya dauki nauyin karatun matashin har zuwa matakin digiri na uku tare da alkawarin bashi aiki kyauta bayan ya kammala karatunsa.

Matashin mai shekaru 20, mazaunin sansanin 'yan gudun hijira (IDP) a Maiduguri, ya zama zakara a gasar musabaqar Alqur'ani da aka gudanar a kasar Saudiyya kwanan nan.

DUBA WANNAN: Daukaka kara: Alkalai 7 da zasu saurari karar Atiku a kotun koli

Goni Adam Muhammad, kawu a wurin matashin, shine ya kawo shi sansanin 'yan gudun hijira daga karamar hukumar Marte kafin ya kammala haddar Alqur'ani.

Wani ma'aikacin gidan rediyo da talabijin na jihar Borno (BRTV), Abdulsalam Mohammed, wanda ya halarci gasar musabaqar da aka yi a birnin Makkah, ya shaidawa Daily Trust cewar nasarar matashin, nasara ce ga jihar Borno da Najeriya baki daya.

Gwamna Zulum ya bawa matashin da ya lashe gasar Alqur'ani kyautar N5m, sabuwar mota da sauransu
Gwamna Zulum yayin bawa matashin da ya lashe gasar Alqur'ani kyautar N5m da sabuwar mota
Asali: Facebook

Gwamna Zulum ya bawa matashin da ya lashe gasar Alqur'ani kyautar N5m, sabuwar mota da sauransu
Idris Abubakar; matashin da ya lashe gasar musabaqar Alqur'ani
Asali: Facebook

Gwamna Zulum ya bawa matashin da ya lashe gasar Alqur'ani kyautar N5m, sabuwar mota da sauransu
Motar da gwamna ya bawa Idris kyauta
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel