Hukumar NDLEA ta kama dilolin kayan maye a hedikwatar jam'iyyar APC a Jigawa

Hukumar NDLEA ta kama dilolin kayan maye a hedikwatar jam'iyyar APC a Jigawa

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) reshen jihar Jigawa ta ce ta kama diloli tare da masu amfani da kayan maye 16 a cikin garin Dutse, babban burnin jihar Jigawa.

Mataimakin shugaban hukumar a jihar Jigawa, Mista Oko Michael, ya tabbatar da kama mutanen ga manema labarai.

Ya ce an kama masu laifin ne a harabar hedikwatar jam'iyyar APC da ke cikin garin Dutse.

Mista Oko ya bayyana cewa jami'an hukumar NDLEA sun kai samame wurin ne ranar Lahadi bayan samun korafi daga jama'a a kan yadda batagari suka mayar da wurin cibiyar sha tare da hada-hadar kayen maye a wurin.

DUBA WANNAN: Kudin yakin neman zabe: Shekarau, Wali da Mansur sun shiga 'tsaka mai wuya'

"Mun kai samame wurin ne bayan mun samu korafi da dama daga wurin jama'a a kan yadda wasu batagari suka mayar da harabar hedikwatar jam'iyyar APC da ke Dutse, babban birnin jiha, ciyar sha da fataucin kayen maye," a cewarsa.

Ya bayyana cewa an samu kullin tabar wiwi yayin da aka kama matasan tare da bayyana cewa za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala binncike.

Sakataren yada labaran jam'iyyar APC a jihar Jigawa, Alahji Nasiru Dahiru, ya tabbatar da kai samamen da jam'an hukumar NDLEA suka yi, amma ya musanta cewa masu laifin mambobin jam'iyyar APC ne.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng