Babbar magana: Majalisar dinkin duniya ta yi kira a kan a gaggauta kawo karshen ta'addanci a Najeriya

Babbar magana: Majalisar dinkin duniya ta yi kira a kan a gaggauta kawo karshen ta'addanci a Najeriya

Agnes Callamard, Wakiliya na musamman da ke aika wa majalisar dinkin duniya (UN) rahoto a kan kisa ba bisa ka'ida ba ya yi Allah-wadai da yawaitar aiyukan ta'addanci a fadin Najeriya.

Da take jawabi yayin taro da manema labarai a Abuja ranar Litinin, Callamard ta ce akwai bukatar daukan matakan gagga wa domin kawo karshen aiyukan ta'addanci da suka yi sanadiyyar salwantar rayukan dubban jama'a a Najeriya.

Najeriya na fama aiyukan ta'addanci masu suna daban-daban da suka hada da; Boko Haram, rikicin makiyaya da manoma, garkuwa da mutane, 'yan bindiga da rikicin mabiya mazhabar Shi'a.

"Hankalina ya tashi matuka da abinda na gani a Najeriya. Akwai bukatar a dauki matakan gagga wa a domin kawo karshen aiyukan ta'addanci da suke kara mamaye Najeriya, musamman a cikin shekaru biyar da suka gabata zuwa yanzu.

DUBA WANNAN: ICPC na daf da kwace miliyan N840 da ta gano a asusun tsohuwar alkaliya daga arewa

"Idan aka bar rikicin da ke faruwa a Najeriya ya cigaba a haka, ba tare da daukan mataki ba, lamarin zai shafi gaba daya kasashen Afrika saboda irin rawar da kasar ke taka wa a nahiyar," a cewar Callamard.

Kazalika, ta yi Allah-wadai da abinda ta kira 'mugunta da cin zali' da 'yan sanda da sojoji ke yi a fadin Najeriya da kuma tsarin 'kama karya'.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng