Ba zan taba yin mataimakin gwamna ba – Dino Melaye

Ba zan taba yin mataimakin gwamna ba – Dino Melaye

- Sanata Dino Melaye ya karyata cewar yana so ya fito a matsayin mataimakin gwamnan wani tsohon gwamnan jihar, Captain Idris Wada

- Melaye yace an shirya bayanin ne domin hana shi zama dan takarar jam’iyyar PDP, a zaben fidda gwani na gwamna da za a gudanar a ranar 3 ga watan Satumba

- Ya nemi jama'a da su yi watsi da batun

Sanata maiwakiltan yankin Kogi ta yamma, Dino Melaye ya karyata cewar yana so ya fito a matsayin mataimakin gwamnan wani tsohon gwamnan jihar, Captain Idris Wada.

A wani jawabi daga hannun hadiminsa a kafofin watsa labarai, Gideon Ayodele, a ranar Alhamis, 29 ga watan Agusta, sanatan ya bayyana cewa an shirya bayanin ne domin hana Melaye zama dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), a zaben fidda gwani na gwamna da za a gudanar a ranar 3 ga watan Satumba.

“Captain Idris Wada ya fadi a zaben da ya gabata, inda ya sha kaye a hannun gwamna mai mulki sannan hakan ba zai yi wani ma’ana ba cewa Dino Melaye, mutumin da ya fi shi dabaru da hangen nesa, zai tsaya a bayan irin wannan dan takara,” cewar jawabin.

A wani rahoton, Legit.ng ta kawo muku cewa kotu ta soke zaben Sanata Dino Melaye mai wakiltan mazabar Kogi ta Yamma na jihar Kogi inda ta bukaci a sake gudanar da sabon zabe kan dalilin kallubalantar nasararsa da akayi a kotu.

A bangarensa, Dino Melaye ya ce ko kadan hakan bai razana shi ba kuma yana da tabbacin cewa nasarar da ya samu tun farko tabbataciya ce.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng