Da duminsa: Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan

Da duminsa: Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan

Labarin da Legit.ng ta samu da yammacin ranar Lahadi daga shafin mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren kafafen sadarwa na zamani, Bashir Ahmad, na nuni da cewa shugan kasa, Muhammadu Buhari, ya tashi zuwa kasar Japan.

A cikin sanarwar da Bashir ya fitar, ya bayyana cewa shugaba Buhari ya bar Abuja zuwa birnin Yokohama na kasar Japan domin wani halartar wani taron kasa da kasa da za a yi a ranar Laraba, 28 ga watan Agusta, 2019.

Za a yi taron ne a kan cigaban kasashen Afrika (CITAD), kuma wannan shine karo na bakwai da aka taba gudanar da taron tun da aka fara yinsa.

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, da takwaransa na jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu da kuma gwamnan jihar Kwara, Abdulrazak Abdulrahman, na daga cikin 'yan rakiyar shugaba Buhari zuwa taron na TICAD7.

Da duminsa: Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan
Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan tare da gwamnonin jihar Borno, Legas da Kwara.
Asali: Twitter

Da duminsa: Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan
Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan
Asali: Twitter

Da duminsa: Shugaba Buhari ya tashi zuwa kasar Japan
Shugaba Buhari kafin ya tashi zuwa kasar Japan
Asali: Twitter

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng