Kamfanoni 15 da za su rinka shigo da man fetur Najeriya a bana

Kamfanoni 15 da za su rinka shigo da man fetur Najeriya a bana

A wani yunkurin na wadatar da kasar nan da man fetur, shugaban kamfanin man fetur na Najeriya, Mele Kolo Kyari, ya ce kamfanin na shirin hada gwiwa da wasu 'yan kasuwanni masu zaman kansu domin tabbatar da ci gaban kasa.

Kamfanin man fetur na Najeriya a ranar Lahadi, 18 ga watan Agustan 2019, ya fidda sunayen kamfanoni 15 da aka bai wa kwantaragin tace danyan man fetur wanda zai wadatar da kasar a bana.

Kyari wanda ke kokarin kara tabbatar da gaskiya a al'amuran kamfanin, ya shaidawa manema labarai na jaridar Premium Times wannan sabuwar wallafa ta sunayen kamfanonin da za su shige gaba wajen gudanar da harkokin man fetur a kasar.

Makonnin kadan da suka gabata, Kyari wanda aka nada jagorancin kamfanin man fetur a watan Yuli, ya ce zai wallafa sunayen wadanda za su gudanar da kwangilar danyen man fetur ta kasar da kuma kamfanonin da suka taki nasarar samun aikin musayar danyan mai na Najeriya da tace shi.

Ga jerin sunayen kamfanonin 15 kamar yadda kakakin kamfanin, Ndu Ughamadu ya bayyana:

1. BP OIL INTERNATIONAL LTD./AYM SHAFA LTD.

2. VITOL SA/CALSON-HYSON

3. TOTSA TOTAL OIL TRADING SA/TOTAL NIG. PLC

4. GUNVOR INTERNATIONAL B.V./AY MAIKIFI OIL & GAS CO. LTD.

5. TRAFIGURA PTE LTD./A. A. RANO NIG. LTD

6. CEPSA S.A.U./OANDO PLC

7. MOCOH SA/MOCOH NIG. LTD.

8. LITASCO SA/BRITTANIA-U NIG. LTD./FREEPOINT COMMODITIES

9. MRS OIL & GAS COMPANY LTD

10. SAHARA ENERGY RESOURCE LTD

11. BONO ENERGY LTD./ETERNA PLC/ARKLEEN OIL & GAS LTD./AMAZON ENERGY

12. MATRIX ENERGY LTD./PETRATLANTIC ENERGY LTD./UTM OFFSHORE LTD./LEVENE ENERGY DEVELOPMENT LTD

13. MERCURIA ENERGY TRADING SA/ BARBEDOS OIL & GAS SERVICES LTD./RAINOIL LTD./PETROGAS ENERGY

14. ASIAN OIL & GAS PTE LTD./ EYRIE ENERGY LTD./ MASTERS ENERGY OIL & GAS LTD/CASIVA LTD

15. DUKE OIL COMPANY INCORPORATED.

KARANTA KUMA: Gwamna Matawalle ya nada sabon shugaban ma'aikatan jihar Zamfara

Sabon shugaban kamfanin ya ce bayyana ayyukan kamfanin da kuma shirin bunkasa harkar cinikayyar man fetur na kasar zai bunkasa zuba jari, wanda a baya a ya durkushe saboda rashin gaskiya.

Jaridar BBC Hausa ta ruwaito cewa, an dai kwashe shekaru ba a wallafa bayanan irin wadanda kwangiloli ba, kuma a cikin shekaru da dama ana yi wa kamfanin kallon wanda ke cike da ayyukan rashawa, lamarin da ya sha musantawa.

Kyari ya ce akwai bukatar farfado da matatun man fetur na gwamnati,wanda ya ce muddin hakan ya tabbata Najeriya za ta iya zamowa mai samar da mai ga nahiyyar Afirka baki daya.

Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel