Za mu ci gaba da hakar mai a Arewa - Shugaban NNPC

Za mu ci gaba da hakar mai a Arewa - Shugaban NNPC

Sabon manajan darakta na Kamfanin man fetur na Najeriya (NNPC), Mista Mele Kolo Kyari, ya bayyana cewa kamfanin zai ci gaba da binciken man fetur ba jib a gani a yankin Arewacin kasar, tare da yankin tafkin Chadi.

Mista Kyari, ya bayyana hakan ne jim kadan bayan tsohon Shugaban kamfanin, Dakta Mai Kanti Baru, ya gabatar da shi a gaban Shugaban kasa Muhammadu Buhari, a fadar Shugaban kasa da ke Abuja.

An tattaro inda yake fadin cewa: “Za mu ci gaba da neman hanyoyin hako mai a yankunan Arewa da sauran yankunan kan iyakar Najeriyar.

“Muna da wuraren da har yanzu ba mu kai ga gano mai ba harma a yankin kudancin kasar, za mu bunkasa hakar mai ta yadda kowa zai amfana da gajiyar hakan shirin za mu aikata hakan, cikin yardar Allah.”

KU KARANTA KUMA: Ku yi watsi da barazanar kungiyar arewa kan Ruga – Fadar Shugaban kasa ga yan Najeriya

A wani labari na daban, Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Laraba, ya amince kashe biliyan N5 a makarantun gaba da sakandire na kasa domin gudanar da bincike a bangarorn ilimi daban-daban.

Hukumar sarrafa kudaden gudanar da aiyuka a makarantun gaba sakandire (TETfund) ce za ta raba kudin ga manyan makarantun.

Babban sakataren hukumar TETFund, Farfesa Suleiman Bogoro, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin rantsar da wani kwamitin da zai gudanar da rabon kudin bayan ya tantance yadda za a raba su.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng