Ministan Shari'a na Najeriya Abubakar Malami ya yi murabus

Ministan Shari'a na Najeriya Abubakar Malami ya yi murabus

Lauyan koli kuma Ministan Shari'a na kasa, Abubakar Malami, ya ce kawowa yanzu kudaden da ma'aikatar sa ta kwakulowa gwamnatin tarayya sun kai kimanin Naira biliyan 270 daga kan Naira biliyan 19.5 da su ke a shekarar 2015.

Malami wanda ya kasance zababben Ministan shugaban kasa Muhammadu Buhari daga jihar Kebbi, ya bayyana hakan ne cikin garin Abuja yayin gabatar da jawaban sa na bankwana na kawo karshen wa'adin sa a matsayin jagoran ma'aikatar shari'a ta kasar nan.

Ministan Shari'a na Najeriya; Abubakar Malami
Ministan Shari'a na Najeriya; Abubakar Malami
Asali: Depositphotos

A cewar wani rahoto daga jaridar Vanguard ta fitar, Malami ya ce gwamnati ta shirya tsaf wajen tabbatar da dawowar kadarorin ta da suka kai kimanin dalar Amurka miliyan 500 daga kasar Faransa, Amurka, Jersey.

Ya yi waiwaiye da Hausawa ke cewa adon tafiya na hobbasan sa yayin dawowa da kasar nan tarin dukiya daga kasar Switzerland ta kimanin Naira miliyan 322.5 da tsohon shugaban kasa Marigayi Janar Sani Abacha ya wawushe.

KARAMTA KUMA: Gwamna Ganduje ya jagoranci musuluntar da Maguzawa 74 a jihar Kano

Malami da ya kasance Ministan shari'a na kasar nan a shekarar 2015 bayan ya karba daga hannun Magajin sa, Muhammad Adoke, ya hikaito kwazon da ma'aikatar sa ta yi cikin tsawon shekaru hudu da suka gabata.

Shakka babu masu sharhi sun shaida cewa hukumar shari'a da ta kasance a karkashin kulawar Malami, ta yi aiki tukuru wajen ba wa gwamnatin tarayya goyon bayan tare da taka muhimmiyar rawar gani a fagen yakin ta na cin hanci da rashawa.

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.android&pid=solomonovlink

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na dandalan sada zumunta a Facebook ko kuma Twitter:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Ku fa'idantu da manhajar mu ta Azumi a wannan wata mai albarka a wannan shafi:

https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel