Manyan alkalai mata guda 8 da sunayen manyan 'yan siyasa da suke aure
Majiyarmu ta binciko muku jerin manyan alkalai mata guda takwas da kuma sunayen mazajen su manyan 'yan siyasa na Najeriya da suke aure
Kwana biyu da suka wuce, alkalin kotun daukaka kara, Mai shari'a Zainab Bulkachuwa, ta ceto kanta daga rikicin karar zabe da take saurara, bayan da jam'iyyar PDP ta taso da zancen cewa mijinta dan jam'iyyar APC ne.
A yau majiyarmu Legit.ng za ta kawo muku jerin manyan alkalai mata da mazajensu wadanda suke manyan 'yan siyasa ne a kasar nan.

Asali: Facebook
1. Mary Odili
Mary Odili ita ma wata shahararriyar alkali ce, matar tsohon gwamnan jihar Rivers Dr. Peter Odili, wanda ya fito takarar shugaban kasa a lokacin mulkin PDP.
2. Zainab Bulkachuwa
Zainab Bulkachuwa, ita ce shugabar kotun daukaka kara ta kasa. Tana auren zababben Sanatan APC na jihar Bauchi, Alhaji Adamu Bulkachuwa.
3. Fati Lami Abubakar
Fati matar tsohon shugaban mulkin soja ne, Gen Abdulsalami Abubakar (Rtd), wanda ya hau mulki bayan mutuwar tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha a shekarar 1998.
4. Binta Nyako
Binta Nyako ta na daya daga cikin manyan alkalai a Najeriya wacce sunanta ya karade kowanne lungu da sako na kasar nan. Binta Nyako ita ce matar tsohon gwamnan jihar Adamawa, Murtala Nyako, wanda yayi mulki daga shekarar 2007 zuwa 2015.
KU KARANTA: An soke hawan sallah a jihar Katsina
5. Eberechi Wike
Eberechi Wike ita ce matar gwamnan jihar Rivers na yanzu, Cif Nyesom Wike.
6. Maryann Anenih
Maryann Anenih ita ce karama a cikin matayen Cif Anthony Anenih, tsohon shugaban jam'iyyar PDP na kasa, wanda aka fi sani da sunan shi na siyasa da Mista Fix-It.
7. Chioma Nwosu-Iheme
Dr. Chioma Nwosu-Iheme alkalin kotun daukaka kara ce. Tayi karatu a bangaren shari'a har ta kai matsayin Farfesa, kuma ita ce mace ta farko da ta fara kaiwa wannan matsayin a Najeriya. Ita ce matar tsohon kwamishinan cigaban karkara, sannan kuma kwamishinan ilimi na jihar Imo.
8. Jumoke Pedro
Jumoke Pedro ita ce alkalin babbar kotun jihar Legas, tana auren tsohon mataimakin gwamnan jihar Legas Femi Pedro.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa nan: Domin karuwa cikin wannan wata mai alfarma na Ramadana
Asali: Legit.ng