Hukumar EFCC ta shigar da karar Bala Mohammed a gaban Kotu

Hukumar EFCC ta shigar da karar Bala Mohammed a gaban Kotu

Yayin da ake saura wata guda cak a rantsar da sababbin gwamnoni da shugaban kasa a Najeriya, EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon-kasa tana neman kama Bala Mohammed.

Kamar yadda labari ya samu zuwa mana, A yau Litinin, 29 ga Watan Mayu ne Sanata Bala Mohammed na jam’iyyar PDP, zai bayyana a gaban kotu, inda hukumar EFCC ta ke zargin sa da wasu manyan laifuffuka har 6.

Hukumar EFCC tana tuhumar gwamnan mai-jiran gado da laifin kin bayyana kadarorinsa, da kuma ba hukuma bayanan karya a game da dukiyar da ya mallaka. Haka kuma ana zargin Bala Mohammed da karbar cin hanci.

Za a gurfanar da Kauran Bauchi ne a babban kotun tarayya da ke Maitama a cikin Garin Abuja, inda zai amsa laifuffuka har 6. Wahab Shittu shi ne Lauyan da EFCC ta sa domin ya binciki gwamnan na jihar Bauchi mai jiran-gado.

KU KARANTA: Atiku ya hango nasara a shari’ar zaben 2019 da yake yi da Buhari

Hukumar EFCC ta shigar da karar Bala Mohammed a gaban Kotu
Ana zargin ‘Dan takarar PDP da ya doke Gwamnan Bauchi da laifuffuka
Asali: Twitter

Bala Mohammed ya bayyana cewa ba komai bane wannan illa cinne ne gwamnatin APC ta ke yi masa, bayan ganin ya doke gwamnan ta a zaben 2019. Mohammed yace ba yau aka saba bincikensa ba, kuma ba ya jin tsoron komai.

Wanda ake tuhuma ya sha alwashin kare kan sa a gaban kotu kamar yadda ya samu nasara shari’ar sa da gwamnatin tarayya kwanaki. Bala Mohammed dai ya rantse sai ya binciki gwamnatin APC idan ya hau mulki a jihar Bauchi.

Tsohon Ministan na babban birnin tarayya Abuja, Sanata Bala Mohammed, ya lashe zaben gwamnan jihar Bauchi da aka yi a watan jiya inda ya doke gwamna mai-ci Mohammed Abubakar na jam’iyyar APC.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel