Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)
Shugaban rundunar soji ta kasa, Laftanal Janar TY Buratai, ya bude sabon katafaren ginin makarantar sojojin 'infantry' da aka yi a cikin hedikwatar soji ta Jaji da ke jihar Kaduna.
Buratai da ragwar manyan hafsoshin rundunar sojin kasa na jihar Kaduna domin halartar wani muhimmin taro da za a yi a cikin satin nan.
Kafin ya wuce zuwa Jaji domin kaddamar da sabon ginin na zamani, Legit.ng ta kawo muku labarin cewar tawagar shugabannin rundunar soji a karkashin jagorancin shugaban rundunar soji ta kasa, Laftanal Janar TY Buratai, sun ziyarci fadar gwamnatin jihar Kaduna da safiyar ranar Laraba.
Mataimakin gwamnan jihar Kaduna, Barnabas Bala Bantex, ne ya karbi Buratai da ragowar shugabannin rundunar sojin.
DUBA WANNAN: Maigadi ya zabi a gina tuka-tuka a kauyensu a kan karbar kyautar gida
A jawabin mataimakin gwamnan, ya gode wa rundunar soji a kan kafa sansani a Kafanchan da Birnin Gwari.
A nasa jawabin, Buratai ya shaida wa mataimakin gwamnan cewar zasu daga darajar sansanin biyu zuwa manyan rundunar sojoji.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng