Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)

Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)

Shugaban rundunar soji ta kasa, Laftanal Janar TY Buratai, ya bude sabon katafaren ginin makarantar sojojin 'infantry' da aka yi a cikin hedikwatar soji ta Jaji da ke jihar Kaduna.

Buratai da ragwar manyan hafsoshin rundunar sojin kasa na jihar Kaduna domin halartar wani muhimmin taro da za a yi a cikin satin nan.

Kafin ya wuce zuwa Jaji domin kaddamar da sabon ginin na zamani, Legit.ng ta kawo muku labarin cewar tawagar shugabannin rundunar soji a karkashin jagorancin shugaban rundunar soji ta kasa, Laftanal Janar TY Buratai, sun ziyarci fadar gwamnatin jihar Kaduna da safiyar ranar Laraba.

Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)
Sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji ta Jaji
Asali: Twitter

Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)
Buratai yayin kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji
Asali: Twitter

Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)
Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji ta Jaji
Asali: Twitter

Buratai ya kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji a Jaji (Hotuna)
Buratai yayin kaddamar da sabon katafaren ginin makaranta a hedikwatar soji ta Jaji
Asali: Twitter

Mataimakin gwamnan jihar Kaduna, Barnabas Bala Bantex, ne ya karbi Buratai da ragowar shugabannin rundunar sojin.

DUBA WANNAN: Maigadi ya zabi a gina tuka-tuka a kauyensu a kan karbar kyautar gida

A jawabin mataimakin gwamnan, ya gode wa rundunar soji a kan kafa sansani a Kafanchan da Birnin Gwari.

A nasa jawabin, Buratai ya shaida wa mataimakin gwamnan cewar zasu daga darajar sansanin biyu zuwa manyan rundunar sojoji.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel