Da duminsa: Ali Nuhu ya maka Adam A Zango a Kotu, duba takardan sammaci
Fittacen jarumin Kannywood, Ali Nuhu ya yi karar Adam A Zango a kotu kan cewa kotu ta shiga tsakaninsa da Zango kuma ya daina ba ta masa suna kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Wannan na dauke ne cikin takardan kirar kara wanda Ali Nuhu ya shigar a kotun USC da ke Fagge a Kano.
Kotun ta bukaci Adam Zango ya gurfana gaban a ranar 15 ga watan Maris na 2019 misalin karfe 8.30.
"Kotu tana kiran ka a kan shari'a da ke a gabanta na neman shiga tsakani a kan bata suna don haka sai ka zo kotu ranar da na ambata a sama," kamar yadda aka rubuta a jikin takardan sammacin.
DUBA WANNAN: Zargin Madigo: Yadda Hadiza Gabon ta titsiye Amina Amal, ta rika zagba mata mari
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng