Satar yara: "Yan sanda sun kama mutane uku a Zuba ta Abuja

Satar yara: "Yan sanda sun kama mutane uku a Zuba ta Abuja

Rubdunar 'yan sanda a birnin tarayya, Abuja, ta ce ta kubutar da wasu yara biyu da ake zargin wasu matasa uku da sace wa a yankin Zuba.

Matasan uku da akama su ne: Nasiru Mohammed mai shekaru 20, Sale Bello mai shekaru 19, da Hassan Audu mai shekaru 20.

Kwamishinan 'yan sandan Abuja, Bala Chiroma, ne ya gabatar da matasan ga manema labarai a Abuja a ranar Laraba.

Ya ce yaran da aka sace; Seke mai shekaru 9 da Rejoice Godwin mai shekaru 7, 'ya'yan mutum daya ne da aka sace ranar 8 ga watan Maris a kauyen Yimi da ke Zuba, sannan an kubutar da su ne a Lambata da ke jihar Neja.

Kwamishinan ya kara da cewa an samu wasu bindigun baushe biyu a wurin matasan yayin da 'yan sanda suka kama su.

Satar yara: "Yan sanda sun kama mutane uku a Zuba ta Abuja
Sifeton rundinar 'yan sanda ta kasa; Adamu Lafiya
Asali: Original

Kazalika, Ciroma ya ce rundunar 'yan sanda a Abuja tayi nasarar kama wasu 'yan fashi biyar da ake zargi da yin sata a wani gida da ke rukunin gidajen 'Sun City' a yankin Galadimawa ta Abuja.

Wadanda aka kama din su ne: Ayuba Isaac mai shekaru 22, Philemon Yohanna mai shekaru 28, Johnson Moses mai shekaru 28, Oduola Dayo mai shekaru 28, da Paul Philip mai shekaru 22.

DUBA WANNAN: Kisan Musulmai 50: An gano kungiyar da maharin New Zealand ke yiwa biyayya

Ya bayyana cewar jami'an 'yan sanda sun kama daya daga cikin 'yan fashin a shataletalen unguwar Galadimawa, yayin da aka kama ragowar abokansa a maboyar su a ranar 3 ga watan Maris.

Ciroma ya ce daga cikin abubuwan da aka samu a wurin 'yan fashin akwai bindigu biyu da alburusai, wani karfe na musamman, wayar hannu da kudi N91,000.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng