An samu gawar wani malamin jami'a a yashe a kasa, bayan kwana hudu ana neman shi

An samu gawar wani malamin jami'a a yashe a kasa, bayan kwana hudu ana neman shi

- An samu gawar wani malamin jami'a a cikin kangon shi ta fara lalacewa, kwanaki hudu bayan an neme shi an rasa

- Rahotanni sun nuna cewa malamin ya kashe kanshi ne, saboda ba wannan ne karo na farko da yayi kokarin kashe kanshi ba

An samu gawar wani malamin jami'a mai suna Patrick Okojie, wanda ke koyarwa a wata jami'a dake karamar hukumar Auchi cikin jihar Edo, an samu gawar tashi ne bayan kwanaki hudu da bacewar shi.

An samu gawar wani malamin jami'a a yashe a kasa, bayan kwana hudu ana neman shi
An samu gawar wani malamin jami'a a yashe a kasa, bayan kwana hudu ana neman shi
Asali: Getty Images

Gawar malamin da aka sameta a wani kangon shi dake Igbira, akan hanyar Igarra/Auchi. Gawar da aka sameta lokacin ta fara lalacewa.

KU KARANTA: Kahutu Rarara: Dalilin da ya sa nayi wakar 'Ta leko ta labe'

Rahotanni sun nuna cewa Okojie ya kashe kanshi shine. Iyalan shi sun shiga wani hali da suka samu labarin mutuwar ta shi, inda suka ce bai bar wata takarda ba da zata nuna cewa shine ya kashe kanshi.

Sai dai kuma rahotanni sun nuna cewa ba wannan ne karo na farko da Okojie ya fara kokarin kashe kanshi ba.

Ya mutu ya bar mata daya da yara uku.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel