Sunayen yan siyasa 18 dake muradin darewa kujerar gwamnan jahar Borno

Sunayen yan siyasa 18 dake muradin darewa kujerar gwamnan jahar Borno

Akalla jam’iyyu arba’in da daya ne suka tsayar da yan takara daban daban da zasu wakilcesu a fafatawar da za’ayi a zaben gwamnan jahar Borno a ranar Asabar, 9 ga watan Maris, kamar yadda kwamishinan hukumar INEC, reshen jahar Borno ya bayyana.

Legit.ng ta ruwaito kwmaishinan mai suna Mohammed Ibrahim ya bayyana haka ne yayin da yake ganawa da manema labaru a ranar Laraba, 6 ga watan Maris, inda yace daga cikin jam’yyu 41 da suka tsayar da yan takara har da APC da PDP.

KU KARANTA: An bude asusun neman taimako dan taimaka ma Atiku ya kai karar Buhari gaban kotu

Bugu da kari, Ibrahim yace akwai yan takarkarun kujerun majalisar dokokin jahar Borno da adadinsu ya kai dari hudu da saba’in da takwas, 478, kamar yadda jam’iyyun suka mika musu.

Daga karshe Ibrahim ya bada tabbacin shirin hukumar zabe mai zaman kanta, INEC na gudanar da ingantaccen zabe a jahar Borno, inda yace daga ranar Alhamis zasu fara aika kayan zaben zuwa kananan hukumomi.

Ga jerin wasu yan takarar gwamnan jahar Borno su goma sha takwas;

APC – Farfesa Babagana Zulum

IDP - Rufai Munguno

SDP - ABBA MODU

PDP – Muhammad Imam

ANRP- - Ahmed Dikwa

ZLP – Ibrahim Mshelia

AD – Mukhtar Abdullahi

ADC – Muhammad Khalajinda

APP - UMAR ALI DIMARI

DPP - YUSUF KACHALLAH

GPN - MOHAMMED SHEHU LAMINU

NPM - ADAMU ALI

NRM - MUSTAPHA UMAR MUSTAFA

PPA - BABAGANA MUSA K

PPN - UMAR MUSTAPHA

UPN - USMAN BABA

UP - ALH. BAKO ALI BARMA

YES - BABAGANA MOHAMMED

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel