Manyan kasashen duniya na kawo wa shugaba Buhari jinjina kan nasararsa, suna kira ga PDP tayi hakuri
- Amurka ta taya shugaban kasa Muhammad Buhari murnar komawar shi kan kajerar sa
- UK ta fahimce cewa al'ummar Najeriya suna da kwarin gwiwa akan sakamakon zaben
-A ranar Laraba ne dai hukumar zabe ta kasa ta bayyana Muhammad Buhari a matsayin wanda ya lashe zaben
Kasar Ingila ta mika sakon taya murnar ta ga shugaban kasa Muhammad Buhari bisa samun nasarar komawa kan kujerar mulki a karo na Biyu.
Ta mika wannan sako ne ta bakin Harriett Baldwin a ranar Laraba inda tace"ina mika sakon taya murna ga shugaban kasa Muhammad Buhari bisa nasarar daya samu na kara komawa kan kujerar sa a karo na biyu".
Akwai kyakkyawar alaka tsakanin UK da Najeriya dama al'ummar kasar baki daya.
Sakamakon da hukumar zabe ta INEC ta fitar yayi daidai da sakamakon da al'ummar da suka kada kuri'ar su suke jira.
GA WANNAN: An kama wata malama da laifin fyade ga wata yarinya a jihar Ikko
'Ta hanyar abokan huldarmu UK ta fahimci cewa yan Najeriya suna da kwarin gwiwa akan sakamakon zaben".
Ministan ta shawarci duk wani wanda wannan sakamako baiyi masa ba dayabi abun cikin nutsuwa.
Sannan ta kara da mika sakon ta'azziyar ta ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wajen zaben.
A ranar Laraba ne dai hukumar zabe ta kasa (INEC) t bayyana shugaban kasa Muhammad Buhari a matsayin wanda ya lashe zaben.
Shafin NAIJ.com Hausa ne ya koma LEGIT.ng Hausa
Latsa kuga sabuwar manhajar Legit.ng Hausa a wayarku ta salula: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Shafukanmu na dandalin sada zumunta sune:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng