Zaben 2019: An tattara sakamakon zabe daga Kananan hukumomi 13 na Jihar Kaduna

Zaben 2019: An tattara sakamakon zabe daga Kananan hukumomi 13 na Jihar Kaduna

Mun sake samun sakamakon zaben shugaban kasa daga jihar Kaduna bayan kananan hukumomin da aka fitar a baya. Yanzu INEC ta bayyana cewa Atiku Abubakar yayi nasara a kananan hukumomi 5.

Zaben 2019: An tattara sakamakon zabe daga Kananan hukumomi 13 na Jihar Kaduna
Atiku ya lashe zabe a wasu Garuruwa na Kudancin Kaduna
Asali: Twitter

An sanar da cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC ne yake jan ragamar kuri’un yankin inda ya samu nasara a kananan hukumomi irin su Ikara, Makarfi, Kudan, Kubau Giwa, Sabon Gari, Soba, da kuma Kauru.

Ga sakamakon zaben yankin nan kamar haka:

Kauru

APC 33, 578

PDP 27,041

Kagarko

APC 16,663

PDP 21,605

Kajuru

APC 7,888

PDP 31,445

Giwa

APC 45,574

PDP 9,838

KU KARANTA: Jam’iyyar PDP ta ji babu dadi a hannun APC a Jihar Katsina

A baya dai kun ji labarin yadda zaben ya kaya a sauran kananan hukumomin jihar da su ka hada da:

Kaura

APC 6,907

PDP 33,647

Ikara

APC 44,021

PDP 14,464

Makarfi

APC: 36,624

PDP:14,494

Kubau

APC: 67,140

PDP: 13,296

KUDAN

APC:30,577

PDP: 11,692

JABA

APC:6,400

PDP:22, 758

Zangon Kataf

APC:10,411

PDP:62,622

Sabon Gari

APC 58,467

PDP 22,644

SOBA

APC 51, 548

PDP 10, 656

KU KARANTA: Danjuma La’ah ya doke Bala Bentex a akwatin cikin Garin Manchok

Mun kuma samu labarin kujerun majalisar tarayya a bangarorin jihar inda Jam'iyyar APC ta ci kujerar Majalisar Soba da kuri'a 30, 398, ita kuma PDP ta samu 14, 382. Hamza Ibrahim ne ya samu galaba a kan Khalid Ibrahim na PDP.

Haka kuma mun ji cewa PDP ta rasa kujerar Majalisar Tarayyar Makarfi a Kaduna. Atiku ya sha kasa ne a yankin tsohon shugaban PDP Ahmad Makarfi inda Sani Shehu Ladan na APC ya doke Ahmed Hassan Jumare a kujerar majalisa.

Dazu nan mu ka ji cewa jam'iyyar APC ta sake samun kujerar majalisar tarayya a Yankin Ikara da Kubau da ke cikin jihar ta Kaduna. APC ta samu kuri'a har 101, 364 inda shi kuma 'dan takarar PDP mai adawa ya samu kuri'a 35, 956.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel