Kamfen: Katsinawa sun yi wa Buhari kara, hotuna
A yau, Alhamis, ne shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da tawagar yakin neman zaben jam'iyyar APC su ka dira a jihar Katsina domin gudanar da kamfen na karshe bayan cikar wa'adin lokacin yakin neman zabe da INEC ta ware wa 'yan takarar kujerar shugaban kasa.
Miliyoyin masoya da magoya bayan shugaba Buhari da jam'iyyar sa, APC sun cika filin taron kamfen din Buhari tun kafin isowar sa.
DUBA WANNAN: Zamfara: APC ta mika sunayen ‘yan takara ga INEC
Shugaba Buhari dan asalin karamar hukumar Daura ne da ke jihar Katsina.
A daidai lokacin da shugaba Buhri ke kalkale yakin neman zaben sa a jihar sa ta haihuwa, babban abokin hamayyar sa, Atiku Abubakar, na can jihar Adamawa yana gudanar da na shi yakin neman zaben na karshe a jihar Adamawa.
Atiku dan asalin karamar hukumar Jada ne da ke jihar Adamawa.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng