Tabarbarewar ilimin firamare a Kaduna ya saka Farfesa zubar da hawaye

Tabarbarewar ilimin firamare a Kaduna ya saka Farfesa zubar da hawaye

Babban rijistara a hukumar kula da ilimin addinin Islama da harshen larabci (NBAIS), Farfesa Muhammad Shafi’u, ya zubar da hawaye saboda tabarbarewar ilimi a makarantun firamarem gwamnati da ke karamar hukumar Zaria, lamarin da ya sa shi yin kira ga gwamna Nasir El-Rufa’I da ya kawo dauki a bangare.

Farfesa Shafi’u, mai rike da mukamin wakilin makarantar Zazzau, ya yi wannan kira ne yayin wani taron tsofin daliban makarantar firamaren Sarki Ja’afaru da ke kofar Gayan a garin Zaria.

Da ya ke gabatar da jawabi a matsayin san a babban bako a wurin taron tsofin dalliban, Farfesa Shafi’u ya zubar da hawaye a kan yanayin lalacewa da makarantar firamaren ke ciki.

Bai kamata a bar tsohuwar makaranta kamar ta Sarki Ja’afaru, da a shekarar 1942 ta kasance daya daga cikin manyan makarantu uku a garin Zaria, ta lalace ba,” a cewar Farfesa Shafi’u.

Tabarbarewar ilimin firamare a Kaduna ya saka Farfesa zubar da hawaye
Malam Nasir El-Rufa'i
Asali: Depositphotos

Bayan ya yi korafi bias halin ko-in-kula da wasu manya a garin Zaria su ka nuna bias lalacewar makarantar, Farfesa Shafi’u ya dauki alkawarin bayar da gudunmawa domin farfado da makarantar.

DUBA WANNAN: Shigar Atiku Amurka alfarma ce ta wucin gadi - Rahoton Reuters

Kazalika, Aminu Ramalan, wakilin dan majalisar dokoki mai wakiltar Zaria, Abbas Tajudden, ya dauki alkawarin bayar da gudunmawa wajen sake gina makarantar.

A matsayin san a mai kaddamar da littafin hotunan tsofin daliban makarantar, Tajudeen ya sayi littafi guda daya a kan N100,000.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel