Ganduje: Kotun Shari'a tayi watsi da karar da aka shigar a kan Jaafar Jaafar

Ganduje: Kotun Shari'a tayi watsi da karar da aka shigar a kan Jaafar Jaafar

- Kotun Shari'a a jihar Kano tayi watsi da karar da wani Dalhatu Shehu ya shigar a kan Jaafar Jaafar bisa wallafa faya-fayen bidiyon Gwamna Abdullahi Ganduje

- Dalhatu Shehu ya shigar da karar ne inda ya ke nema Jaafar Jaafar ya biya Naira Biliyan 3 a kan abinda ya kira bidiyon karya da aka wallafa domin cin mutuncin Gwamna Ganduje

- Sai dai daga bisani Dalhatu Shehu ya janye karar wadda hakan yasa Alkalin kotun, Mohammed Kademi ya yi watsi da karar

Wata babban kotun Shari'a da ke zamanta a Goron Dutse a jihar Kano tayi watsi da karar da wani Dalhatu Shehu ya shigar a gabanta inda ya ke neman babban Editan Daily Nigerian, Jaafar Jaafar ya gurfana a gaban kotun a kan wallafa bidiyon da ake zargin rashawa Gwamna Abdullahi Ganduje ya ke karba.

Ganduje: Kotun Shari'a tayi watsi da karar da aka shigar a kan Jaafar Jaafar
Ganduje: Kotun Shari'a tayi watsi da karar da aka shigar a kan Jaafar Jaafar
Asali: Twitter

A watan Oktoban 2018 ne Daily Nigerian ta wallafa wasu faya-fayen bidiyo da ke ake ikirarin Gwamna Ganduje ne ke karbar cin hanci na daloli daga hannun wani dan kwangila.

DUBA WANNAN: NJC ta kammala taron gaggawa, tayi hukunci a kan Muhammad da Onnoghen

A Nuwamban 2018 ne Ganduje ya shigar Jaafar Jaafar kara inda ya ke neman a biya shi Naira Bilyan 3 saboda wai 'yadda bidiyon karya da niyyar cin mutuncin gwamnan da bata masa suna.

Duk da cewa Gwamnan ya shigar da kara a babban kotun da ke jihar, wani lauya da ke biyaya ga Ganduje mai suna Dalhatu Shehu ya shigar da wata karar a babban kotun Shari'ar a makon da ta gabata.

Da farko wanda ya shigar da karar ya ce akwai bukatar Jaafar ya gurfana a gaban kotun ya yi rantsuwa da Alkur'ani mai girma a ranar 29 ga watan Janairu.

Amma a lokacin sauraron karar ya yi a ranar Talara, Alkalin kotun, Mohammed Kademi ya yi watsi da karar inda ya ce wanda ya shigar da karar ya janye.

Lauya mai kare Jaafar, Audu Bulama-Bukarti ya nemi kotu ta bashi cikaken bayanin yadda aka janye karar kuma kotun ta amsa wannan roko nasa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164