Osun, Ondo, Ekiti da sauran Jihohin da babu zaben Gwamna a bana
- Akwai wasu Gwamnonin Jihohin da ba tare da su za ayi zaben 2019 ba
- Wadannan jihohi sun hada da irin su Kogi, Ondo da kuma Jihar Ekiti
- Dalili shi ne Gwamnonin Jihohin ba su kammala wa’adin su ba tukuna
Yayin da ake shiryawa babban zaben 2019, mun kawo maku jerin gwamnonin da za su cigaba da mulki har bayan 2019 inda za a gudanar da sabon zabe a jihar. Legit.ng Hausa ta kawo maku jerin wadannan jihohi a Najeriya:
1. Jihar Osun
Kwanan nan ne aka yi sabon zabe a jihar Osun inda ‘Dan takarar APC Adegboyega Oyetola ya doke ‘Dan takarar PDP watau Sanata Ademola Adeleke. Sai a shekarar 2022 ne za a sake zabe a jihar.
2. Jihar Ekiti
Ba da dadewa bane dai tsohon Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi ya sake dawowa kan kujerar sa bayan ya doke PDP a zaben gwamna da aka yi a tsakiyar bara. A 2019 ba za ayi zaben sabon gwamna a Ekiti ba.
3. Jihar Ondo
A karshen 2016 ne aka yi zaben sabon gwamna a jihar Ondo bayan cikar wa’adin Olusegun Mimiko. Rotimi Akeredolu ne yayi nasara a zaben don haka sai a karshen shekara mai zuwa za sake zaben gwamna a jihar.
KU KARANTA: Gwamnan Borno da 'Dan takaran APC sun kwana a kusa da Garin Baga
4. Jihar Edo
A cikin shekarar 2016 ne Adams Oshiomhole ya sauka daga kujerar gwamna inda ‘dan takarar sa na APC watau Godwin Obaseki ya dare kan kujerar. A cikin watan Satumban 2020 ne za a zabi sabon gwamna a jihar ta Edo.
5. Jihar Anambra
Willie Obiano ya sake lashe zaben kujerar gwamnan Anambra ne a daf da karshen 2017. Gwamnan zai kammala wa’adin sa ne a 2021, inda sai a wannan lokaci ne za a sake gudanar da sabon zaben gwamna a jihar.
6. Jihar Bayelsa
A Junairun 2016 ne gwamna Seriake Dickson ya lashe zaben Bayelsa inda ya koma kan kujerar sa. Gwamnan ya tashi da kuri’a 134,998 ne a zabe. Jihar ba ta cikin inda za ayi zaben gwamna har sai a shekarar 2020.
7. Jihar Kogi
Ba za ayi sabon zaben gwamna a jihar Kogi a farkon 2019 ba domin kuwa Yahaya Bello ya gaji zaben da yayi nasara ne a karshen 2015, inda kuma aka nada sa kan mulki a farkon 2016. A Nuwamban bana za ayi zabe a jihar.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT
Asali: Legit.ng