Sojoji za su kaddamar da atisayen Rawar Gansheka III a jihar Kebbi

Sojoji za su kaddamar da atisayen Rawar Gansheka III a jihar Kebbi

A ranar Talata 3 ga watan Janairun 2019 ne za ta kaddamar da atisayen 'Operation Python Dance III' a jihar Kebbi da ke Arewa maso yammacin Najeriya a cewar shugaban hafsin sojojin Najeriya, Laftanat Janar Tukur Buratai.

A yayin da ya bayar da wannan sanarwar a jihar Sokoto, Buratai ya ce barayin shanu da 'yan ta'adda suna yiwa al'ummar yankin barazana.

"Barayin shanu da 'yan ta'adda sunyi sanadiyar rasuwar mutane da dama a yankin Arewa maso yamma, dole a taka musu birki."

Sojoji za su kaddamar da atisayen Rawar Gansheka III a jihar Kebbi
Sojoji za su kaddamar da atisayen Rawar Gansheka III a jihar Kebbi
Asali: Depositphotos

DUBA WANNAN: Fallasa : Dan Boko Haram ya tona asirin yadda suke kai harin bam din Nyanya

Shugaban sojin ya ce ya yi imanin dakarun sojin Najeriya za su iya kawo karshen kashe-kashen sai dai duk da hakan ya ce hukumar sojin za ta cigaba da sake bawa jami'an ta horo lokaci zuwa lokaci.

A cewar Buratai, horo shine ke tabbatar da kwarewa a aiki saboda haka rundunar sojin Najeriya ta ke mayar da hankali a kan bawa dakarun ta horo.

Ya kuma yi kira ga dakarun sojojin su kyautata alakarsu da al'umma farar hula da ke yankin a yayin gudanar da atisayen na Operation Python Dance 3 a yankin na Arewa maso yammacin Najeriya.

Buratai ya kuma ja kunnen sojojin su san inda iyakarsu ta ke a yayin gudanar da atisayen da Operation Python Dance 3 saboda gujewa fadawa tarkon makiya a yayin da suke kokarin tabbatar ta tsaro a kasa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164