Dakarun Soji sunyi nasarar kashe mata 'yan kunan bakin wake uku

Dakarun Soji sunyi nasarar kashe mata 'yan kunan bakin wake uku

- Dakarun sojin Najeriya sunyi nasarar kashe 'yan kunar bakin wake uku a ranar Lahadi 30 ga watan Disambar 2018

- Dakarun Sojin kuma sun kwace Rocket Propelled Grenade (RPG) guda daya da rigar bam

A ranar Lahadi, 30 ga watan Disamba ne Dakarun Sojin Najeriya suka kashe wasu mata uku 'yan kunan bakin wake a kauyen Kubtara da ke karamar hukumar Dikwa na Jihar Borno a yayin da suke sintiri.

Sanarwar da ta fito daga mataimakin Direktan hulda da jama'a na Rundunar Operation Lafiya Dole, Kwanel Onyema Nwachukwu a ranar Litinin ta ce sojojin sun kwace Rocket Propelled Grenade da rigar bam bayan kashe 'yan kunar bakin waken.

Dakarun Soji sun kashe mata 'yan kunan bakin wake uku
Dakarun Soji sun kashe mata 'yan kunan bakin wake uku
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Da dumi-dumi: Boko Haram ta sake kai hari garin Buni Gari

Nwachukwu ya ce hafsin hafsoshin Najeriya, Laftanat Tukur Buratai ya yabawa dakarun sojin bisa nasarar da suka samu a kan 'yan ta'addan.

Buratai ya bukaci sojojin su cigaba da kara kwazo kuma su kasance cikin shiri a ko yaushe domin ganin sun kawar dukkan sauran 'yan ta'addan da suka rage.

A wani rahoton, hukumar Soji ta yi kira da al'umma suyi watsi da wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke haska wani soja yana korafi a kan rashin isasun kayan aiki inda su kace ba haka lamarin ya ke a yau ba.

Direktan yada labarai na Soji, Brig. Janar Sani Usman ya ce bidiyon tsoho ne kuma abubuwan tuni sun canja a halin yanzu.

"Wannan ba gaskiya bane saboda anyi bidiyon ne tun shekarar 2014 saboda haka ba shi da tasiri a yanzu.

"Muna kira da al'umma suyi watsi da wannan faifan bidiyon," inji Usman.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel