Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai sake lashe zaben 2019 – Olagoke

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai sake lashe zaben 2019 – Olagoke

- Wani Malamin addini, Sabit Olagoke yace Buhari ne zai ci zaben 2019

- Babban Limamin yace Jam’iyyar PDP za ta ba Atiku Abubakar kunya

- Malamin ya kuma gargadi masu neman tada fitina su da su sake tunani

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai sake lashe zaben 2019 – Olagoke
Sheikh Olagoke yace Buhari zai tika Atiku Abubakar da kasa a badi
Asali: Facebook

Babban Limamin Shafaudeen Islam watau Sabit Olagoke ya fito ya bayyana cewa tsohon mataimakin shugaban kasar nan, Alhaji Atiku Abubakar, ba zai yi nasara a zaben 2019 ba. Olagoke yace jam’iyyar PDP ce za ta ba Atiku kunya a zaben na badi.

Sheikh Sabit Olagoke wanda yana cikin Malaman da ake ji da shi a Kasar Yarbawa yake cewa duk da karfin Atiku Abubakar, Buhari ne zai koma kan karagar mulki a 2019. Malamin ya kuma bayyana abubuwa da dama da za su faru a shekarar 2019.

KU KARANTA: Atiku na kulle-kullen shigowa da makudan kudi domin zaben 2019

Farfesa Sabit Olagoke ya kuma kara da cewa, wasu mutane su na da shirin tada fitina a zaben 2019. Shehin yace duk masu wannan mugun nufi, ba za su kwana lafiya ba. Fitaccen Malamin yayi duk wannan jawabi ne a Garin Ibadan, a Jihar Oyo.

Olagoke ya kuma yi magana game da sha’anin tsaro a Najeriya, inda yace sai an kara dagewa da addu’a a 2019. Malamin ya nuna cewa tattalin arzikin Najeriya da kuma harkar ilmi zai bunkasa a 2019. Malamin yace za a cigaba har a harkar wasanni.

Farfesan wanda ya taba rike mukami a wata babbar Makaranta da ke Garin Ilaro a Jihar Ogun ya koka da irin kudin da ake warewa harkar ilmi a kasafin Najeriya. Farfesan yace abin da ake batarwa yayi kadan idan aka duba sharudan Hukumar UNESCO.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel