Gwamnan APC ya maka Sufeta Janar na 'yan sanda a kotu, ya nemi a biya shi N1bn

Gwamnan APC ya maka Sufeta Janar na 'yan sanda a kotu, ya nemi a biya shi N1bn

Gwamna Rochas Okorocha na jihar Imo ya yi karar sufeta janar na 'yan sanda Ibrahim Idris saboda bincike gidansa da jami'an yan sanda su kayi a jihar Plateau ba tare da izinin kotu ba.

A yayin da ya ke shigar da karar a gaban Alkali Musa Karya na babban kotun tarayya da ke Jos, gwamnan ya ce bincike a gidansa ba tare da izinin kotu ba ya keta hakkinsa na dan adam.

Gwamnan ya bukaci kotu ta tilastawa 'yan sandan biyansa N1.25 biliyan domin keta haklinsa a akayi.

Gwamnan APC ya maka EFCC da IGP Idirs kara a kotu, ya nemi a biya shi N1bn
Gwamnan APC ya maka EFCC da IGP Idirs kara a kotu, ya nemi a biya shi N1bn
Asali: Twitter

A cikin karar da ya shigar, Okorocha ya yi karar kwamishinan 'yan sanda na jihar Plateau, Hukumar Yaki da Rashawa (EFCC) da Attoney Janar kuma Ministan Shari'ah na kasa.

DUBA WANNAN: 'Yan kasuwa sun yiwa El-Rufai ihu, sunyi watsi da tayin da ya yi musu

Lauyan gwamnan, Markus Saleh (SAN) ya sanar da kotun cewa a ranar 3 ga watan Mayun shekarar 2018 ne aka kai samame gidan wanda ya ke karewa.

Ya yi ikirarin an tsare iyalansa da masu aiki a gidansa ba bisa kan ka'ida ba lokacin da ake bincike a gidan.

Hakan yasa Okorocha ke rokon kotun ta ayyana cewar samamen da aka kai gidansa ba bisa kan ka'ida bane saboda babu izinin yin hakan daga kotu.

Ya kuma roki kotun ta haramtawa hukumomin tsaro bincika gidajensa da ke sassan kasar nan a gaba.

Bayan sauraron karar, Alkalin kotun, Justice Kurya ya daga cigaba da shari'ar zuwa ranar 24 ga watan Janairun shekarar 2019.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164