Manyan ayyukan more rayuwa 5 da Buhari yayi ma jama’an Legas

Manyan ayyukan more rayuwa 5 da Buhari yayi ma jama’an Legas

Kamar yadda ake tsammani daga wajen kowanne shugaban na game da gudanar da ayyukan cigaba ga jama’ansa, haka ne tsammanin da yan Najeriya ke da shi akan Shugaban kasa Muhammadu Buhari, wanda ya dare madafan iko a ranar 29 ga watan Mayu.

Daga cikin jihohin Najeriya masu muhimmanci akwai jahar Legas, jahar da tafi kowace jaha arziki a Najeriya, kuma jaha ta biyu wajen yawan jama’a a Najeriya, bayan jahar Kano, kaar yadda alkalummar hukumar kidaya suka nuna.

KU KARANTA Hadarin jirgin sama a kasar Ingila ta halaka wani mai mallakin kungiyar kwallon kafa ta Leicester

Manyan ayyukan more rayuwa da Buhari ya yi ma jama’an Legas
Aikin layin dogo
Asali: Facebook

Haka zalika jahar Legas na da muhimmanci a siyasance, kusan ita ce daya tilo da ta kwashe shekaru 16 tana karkashin jam’iyyar adawa, ma’ana jam’iyyar PDP bata taba mulkar jahar ba, kuma da tsohon gwamnan jahar, Tinubu aka kafa jam’iyyar APC.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya samu kuri’u dubu bakwai da casa’in da biyu da dari hudu da sittin a yayin zaben shekarar 2015, wanda shine sakamako mafi kyauwu da Buhari ya taba samu a jahar tunda ya fara tsayawa takara.

Manyan ayyukan more rayuwa da Buhari ya yi ma jama’an Legas
Aikin titin
Asali: Facebook

Wasu daga cikin manyan ayyukan da gwamnatin shugaba Buhari ta yi a jahar sun hada da;

Mika tsohon fadar gwamnatin kasa ga gwamnatin jahar Legas

Aikin gina hanyar rukuni na daya da na biyu na babban titin Legas zuwa Ibadan

Aikin gina layin dogo mai tsawon kilomita 151 daga Legas zuwa Ibadan

Aikin sanya wuta a kafatin shagunan dake kasuwar Sura

Daukan dubun dubatan matasa aiki a karkashin N-Power

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng