Yadda Atiku da El-Rufai suka yi rikici kan kudin gudummawar takarar Buhari

Yadda Atiku da El-Rufai suka yi rikici kan kudin gudummawar takarar Buhari

- Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, sun hade da Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufai a wani shirin gidan rediyo

- Sun hadu ne a wani shiri mai suna "Dimokaradiyya a yau" wanda muryar Amurka ta shirya

- Atiku ya bar APC ne saboda jam'iyyar da gwamnoni sun amince da zarcewar Buhari

Yadda Atiku da El-Rufai suka yi rikici kan kudin gudummawar takarar Buhari
Yadda Atiku da El-Rufai suka yi rikici kan kudin gudummawar takarar Buhari
Asali: UGC

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, sun hade da Malam Nasiru Elrufai a wani shiri na gidan rediyo don warware wasu maganganu na jam'iyyar PDP da APC.

Mutanen biyu sunyi Karo ne a shirin "Dimokaradiyya a yau" wanda gidan rediyon muryar Amurka ta shirya a sashen ta na hausa.

Sunyi magana ne akan dalilin da Atiku ya bar APC da kuma cewa Atiku ne ya dau nauyin yakin neman zaben Buhari a 2015.

A cewar Elrufai, Atiku ya bar jam'iyyar APC ne saboda ya gane jam'iyyar da gwamnoni sun amince da zarcewar Buhari a 2019.

DUBA WANNAN: Boka ya kashe mayya

Idan zamu tuna Atiku yace saboda Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari tayi watsi dashi ne duk da rawar ganin da ya taka a yakin neman zabe a 2015.

Amma Elrufai ya kalubalanci Atiku da ya bada shaidar tallafin kudi da yake ta ikirarin ya bada yayi yakin neman zaben Buhari a 2015.

Kamar yanda yace, Atiku ya bar APC ne saboda dalilin kanshi ba wai Don dalilan da ya zayyano ba.

Elrufai yace koda Buhari ba zai tsaya a 2019 ba, toh jam'iyyar bazata ba Atiku tikitin neman shugabancin kasa ba saboda tsohon gwamnan Kano kuma Sanata a yanzu Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ne yake biye da Buhari a zaben fidda gwani a 2015.

"Mu a APC mun dade da sanin cewa Atiku zai bar jam'iyyar zuwa PDP, mun kuma godewa Ubangiji da yasa ya bar jam'iyyar, "Inji Elrufai.

Sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa damu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng