Yadda Atiku da El-Rufai suka yi rikici kan kudin gudummawar takarar Buhari
- Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, sun hade da Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufai a wani shirin gidan rediyo
- Sun hadu ne a wani shiri mai suna "Dimokaradiyya a yau" wanda muryar Amurka ta shirya
- Atiku ya bar APC ne saboda jam'iyyar da gwamnoni sun amince da zarcewar Buhari
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, sun hade da Malam Nasiru Elrufai a wani shiri na gidan rediyo don warware wasu maganganu na jam'iyyar PDP da APC.
Mutanen biyu sunyi Karo ne a shirin "Dimokaradiyya a yau" wanda gidan rediyon muryar Amurka ta shirya a sashen ta na hausa.
Sunyi magana ne akan dalilin da Atiku ya bar APC da kuma cewa Atiku ne ya dau nauyin yakin neman zaben Buhari a 2015.
A cewar Elrufai, Atiku ya bar jam'iyyar APC ne saboda ya gane jam'iyyar da gwamnoni sun amince da zarcewar Buhari a 2019.
DUBA WANNAN: Boka ya kashe mayya
Idan zamu tuna Atiku yace saboda Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari tayi watsi dashi ne duk da rawar ganin da ya taka a yakin neman zabe a 2015.
Amma Elrufai ya kalubalanci Atiku da ya bada shaidar tallafin kudi da yake ta ikirarin ya bada yayi yakin neman zaben Buhari a 2015.
Kamar yanda yace, Atiku ya bar APC ne saboda dalilin kanshi ba wai Don dalilan da ya zayyano ba.
Elrufai yace koda Buhari ba zai tsaya a 2019 ba, toh jam'iyyar bazata ba Atiku tikitin neman shugabancin kasa ba saboda tsohon gwamnan Kano kuma Sanata a yanzu Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ne yake biye da Buhari a zaben fidda gwani a 2015.
"Mu a APC mun dade da sanin cewa Atiku zai bar jam'iyyar zuwa PDP, mun kuma godewa Ubangiji da yasa ya bar jam'iyyar, "Inji Elrufai.
Sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa damu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng