An rataye mujahidai a Misra bayan sun saka bam a coci ya kashe kiristoci

An rataye mujahidai a Misra bayan sun saka bam a coci ya kashe kiristoci

- Wata kotu a kasar Masar ta yankewa mutane 17 hukuncin kisa

- Sannan kotun ta kara yankewa wasu mutum 19 daurin rai da rai a gidan kaso

- A watan Nuwambar bara kungiyar IS ta hallaka mutane sama da 300

An rataye mujahidai a Misra bayan sun saka bam a coci ya kashe kiristoci
An rataye mujahidai a Misra bayan sun saka bam a coci ya kashe kiristoci
Asali: Facebook

Wata kotu a kasar Masar ta yankewa wasu mutane 17 hukuncin kisa inda ta kara yankewa wasu mutum 19 hukuncin daurin rai da rai da wasu 10 wadanda zasuyi shekaru 10 zuwa 15 a gidan kaso bisa laifin tada bama bamai.

A shekarar 2016 da 2017 mutane 74 ne suka rasa rayukan su a dalilin hare hare da aka kai musu a kasar ta Masar.

A watan Nuwambar bara kungiyar IS ta hallaka mutane sama da 300 a hare haren da takai.

Tunda kasar ta ture gwamnatin Shugaba Muhammed Morsi a 2013 suka fama da kashe kashen Sojoji da 'yansanda a sanadiyyar jihadin da shuwagannin kungiyar Muslim Brotherhood suka kira a tashi ayi a kasar.

DUBA WANNAN: Kotu: @MBuhari na da damar kwace kadarorin 'barayin PDP'

Shi dai Muhammad Mursi, dama can gwamnatin Mubarak ta yanke masa hukuncin daurin rai-da-rai a kurkuku saboda zafin ra'ayin Islama.

Ya haure daga kurkuku ne bayan da masu zanga-zanga suka hambare gwamantin ta Hosni Mubarak da 'ya'yansa a 2011.

Sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa damu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng