Kungiyar yan Najeriya dake zaune a kasar Amurka sun bukaci a bari su biya kudinfansar Leah Sharibu

Kungiyar yan Najeriya dake zaune a kasar Amurka sun bukaci a bari su biya kudinfansar Leah Sharibu

- Kungiyar yan Najerya mazauna Amurka sun bukci gwamnati ta bari su iya kudin fansar Leah Sharibu

- Yan ta'addan Boko Haram sun yi barazanar kashe Leah nan da wata guda

- Leah Sharibu ta kasance yar makarantar Dapchi da ta rage a hannun yan ta'addan

Wata kungiyar yan Najeriya mazauna Amurka ta yi zanga-zanga akan barazanar kashe Leah Sharibu da yan ta’addan Boo Haram suka yi inda suka bukaci gwamnatin tarayya da ta bari kungiyoyin dake da ra’ayin biyan kudin fansa domin a sake a suyi.

Kungiyar tayi zargin cewa ta nemi majalisar dinkin dunya ta san baki, lokacin da a samu labarin shirin kashe ta da yan Boko Haram ke yunkurin yi amma suyi korafin cewa babu abunda akayi akai.

Kungiyar yan Najeriya dake zaune a kasar Amurka sun bukaci a bari su biya kudinfansar Leah Sharibu
Kungiyar yan Najeriya dake zaune a kasar Amurka sun bukaci a bari su biya kudinfansar Leah Sharibu
Asali: Depositphotos

Sunce hankalinsu ya tashi matuka da suka samu labarin kashe daya daga cikin ma’aikatan bayar da agaji, Saifura Ahmed da yan ta’addan suka yi.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa kungiyar yan ta’addan Boko Haram sun yi barazanar kashe Leah Sharibu, yan makarantar Dapci dake jihar Yobe guda daya tilo da ta saura a hannunsu cikin 119 da aka sace a watan Fabrairu.

Barazanar na zuwa ne yayinda gamayyar kungiyar Boko Haram suka kashe Saifura Ahmed, daya daga cikin ma’aikatan agaji uku da aka sace a Rann, karamar hukumar Kala Balge.

KU KARANTA KUMA: Yan shi’a sun yi zanga-zanga a Kaduna duk da haramcin da gwamnati ta sanya kan haka (hotuna)

A cewar shafin The Cable, an sace Ahmed ne a lokaci wata mamaya da aka kai sansanin soji a yankin a ranar 1 ga watan Maris.

Akalla sojoji hudu, jami’an yan sanda da ma’aikatan hukumar agaji uku aka kashe a harin.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng