Tawagar gwamnan APC tayi hatsari a hanyar zuwa Abuja

Tawagar gwamnan APC tayi hatsari a hanyar zuwa Abuja

Hukumar Kiyaye Hadura na kas FRSC ta ce wasu motocci cikin tawagar gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi sun yi mummunan hastsari a hanyar Abuja a yau Litinin.

Secta Kwamanda na babban birnin tarayya Abuja, Mr Wobin Gora, ne ya tabbatarwa Tribune Online afkuwar lamarin a Abuja.

Gora ya ce bai gama samun cikaken bayanin hatsarin ba amma ya tabbatar da cewa gwamnan baya cikin tawagar da lokacin da hatsarin ya afku.

Tawagar gwamnan APC tayi hatsari a hanyar zuwa Abuja
Tawagar gwamnan APC tayi hatsari a hanyar zuwa Abuja
Asali: UGC

Wani shaidan ido, ya shaidawa majiyar Legit.ng cewa hatsarin ya afku ne saboda gudun fitan hankali da direbobin motoccin da ke ayarin gwamnan ke yi.

DUBA WANNAN: Mai gadi ya nemi al'auransa ya rasa bayan karbar kudin dan siyasa (Bidiyo)

A wata rahoton, Legit.ng ta gwamna jihar Kogi, Yahaya Bello tare da tawagarsa suna daya daga cikin wanda suka kwashe suka gamu da masu zanga-zanga da suka rufe titin Abuja zuwa Lokoja a hanyarsa ta zuwa Abuja domin ganawa da shugaba Buhari.

A cewar, Akinti Onyegbule, sakataren yada labarai na gwamnan jihar Kogi, direbobin tankan sun fara zanga-zangan ne bayan wani soja ya harbi tayoyin wata tanka.

Ya ce gwamnan ya kwashe kusan sa'a guda yana sulhu tsakanin direbobin da soji kafin masu zanga-zangan suka hakura suka janye motocinsu daga titin

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164