Muhimman abubuwa 8 da ya kamata ku sani game da sabuwar Ministan Kudi, Zainab Ahmed

Muhimman abubuwa 8 da ya kamata ku sani game da sabuwar Ministan Kudi, Zainab Ahmed

A jiya, Juma'a 15 ga watan Satumba ne shugaba Muhammadu Buhari ya amince da murabus din tsohuwar Ministan Kudi, Kemi Adeosun bayan an kwashe watanni ana cece-kuce kan zarginta da gabatar da certificate din kammala hidimar kasa ta bogi.

Shugaban kasa ya godewa ministan bisa gudunmawar da ta bayar a lokacin aikin ta tare da yi mata fatan alheri a ayyukan da za ta yi a gaba.

Ba tare da bata lokaci ba, shugaban kasa ya umurci karamar ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsare na kasa, Zainab Ahmed ta maye gurbin Kemi Adeosun a matsayin ministan Kudi.

Ga wasu muhimman abubuwa 8 da ya dace ku sani a kan Zainab Ahmed.

Muhimman abubuwa 8 da ya kamata ka sani game da sabuwar Minitsan Kudi, Zainab
Muhimman abubuwa 8 da ya kamata ka sani game da sabuwar Minitsan Kudi, Zainab
Asali: Depositphotos

1) An haifi Zainab Shamsuna Ahmed ne a 1963 a jihar Kaduna.

2) Ta kammala karatun digiri na farko daga Jami'an Ahmadu Bello da ke Zaria a 1981 kana ta yi karatun digiri na biyu a fanin nazarin kasuwanci (MBA) a Jami'ar Jihar Ogun da ke Ago Iwoye.

3) Ta fara aiki a matsyasin Akanta a shekarar 1982 a M'aikatar Kudi na jihar Kaduna kuma daga baya ta koma Kamfanin Sadarwa na Kasa (NITEL).

4) A 1995, tayi aiki a sassa daban-daban har ta samu karin girma zuwa matsayin mataimakiyar manaja (DGM)

DUBA WANNAN: Wani Sanata ya bukaci kotu ta aika Saraki gidan yari

5) A shekarar 1995, an nada ta babban sakatariya a Nigeria Industries Transparency Initiative

6) Kafin a nada ta Ministan Kudi na kasa, ita ce Karamar Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsare na Kasa.

7) Ita mamba ce ta Kungiyar Akanta na Najeriya (ANAN) kuma mamba a kungiyar Cibiyar Haraji na Najeriya.

8) A watan Mayun 2009, an nada ta babban manajan Kamfanin Saja Jari na Jihar Kaduna. An kuma nada ta mamba na Kwamitin masu bayar da shawarwari a NEITI.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164