Farashin wasu kayayyaki a kasuwa ya yi tashin gwauron zabi bayan watanni 18 da faduwa

Farashin wasu kayayyaki a kasuwa ya yi tashin gwauron zabi bayan watanni 18 da faduwa

A ci gaba da duba yanayin farashin kayayyaki a kasuwannin kasar nan, Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da wani sabon rahoto a ranar Juma'a, 14 ga watan Satumba, in ta bayyana cewa farashin wasu kayyaki a kasar ya yi tashin gwauron zabi.

A watan Janairun shekara ta 2017 ne farashin kayayyakin ya dai-daita, wanda ya sanya tattalin arzikin kasar ya habbaka, sai dai bayan watanni 18 farashin kayayyakin ya sake tashi, wanda masana ke kallon hakan a matsayin barazana ga kasuwanci da tattalin arzikin kasar.

KARANTA WANNAN: Saboda in ceci rayukan jama'a yasa aka ganni rike da kwalbar giya ina aiki - Dan sanda

A cewar rahoton, farashin kayayyaki da kuma gudanar da ayyukan su a watan Augusta, ya haura daga kashi 11.14% zuwa kashi 11.23%.

Farashin wasu kayayyaki a kasuwa ya yi tashin gwauron zabi bayan watanni 18 da faduwa
Farashin wasu kayayyaki a kasuwa ya yi tashin gwauron zabi bayan watanni 18 da faduwa
Asali: Instagram

"Kididdigar Farashin kayayyakin da jama'a suka fi saye, (CPI) shekara zuwa shekara ya haura da kashi 11.23% a wannan watan na Augusta. Hakan ya sa farashin ya karu da kashi 0.09 idan aka alakanta shi da farashin watan Yulin 2018 (kashi 11.14), wanda hakan ta faru a cikin watanni 18 daga dai-daita farashin," a cewar rahoton.

Rahoton ya ce: "An samu hau-hawar farashin ne a sashen COICOP wanda ya ke a sahun farko na kididdigar. Idan aka duba kididdigar wata zuwa wata, sashen farko na farashin kididdigar ya karu da kashi 1.05 a watan Augustar 2018, la'akari da faduwarsa a watan Yulin 2018, in da aka samu kashi 1.13."

A wani labarin:

Wata babbar cibiyar bincike da kuma fitar da rahoto kan muhimman abubuwa da suka shafi rayuwar kasashe, Forbes Africa, ta bayyana Nigeria a matsayin kasar da ta zamo zakaran gwajin dafi bayan da ta zarce sauran kasashen Afrika a fannin tattalin arzikin kasa a wannan shekarar ta 2018.

A baya bayan nan ne gwamnatin tarayya da sauran gwamnatocin kasar suka samu akalla zambar miliyan 7 (N7tn) a cikin watanni 11, kamar dai yadda rahoton Forbes ya bayyana.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng