Babbar magana: Jonathan ya saka ayar tambaya a kan lafiyar hankalin Oshiomhole

Babbar magana: Jonathan ya saka ayar tambaya a kan lafiyar hankalin Oshiomhole

- Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya saka ayar tambaya a kan lafiyar hankalin shugaban jam’iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole

- Jonathan ya yi wannan kalami ne a matsayin martani ga Oshiomhole a kan batun zargin sayen kuri’u lokacin zabe

- Tsohon shugaban kasar ya ce Oshiomhole na yin barin zance ne saboda matsalolin da suka dabaibaye ofishinsa

Tsohon shugaban kasa Goodluck jonathan ya saka alamar tambaya a kan lafiyar hankalin shugaban jam’iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole. Jonathan na wannan kalami ne a matsayin martini ga kalaman Oshiomhole na cewar a lokacin mulkinsa ne aka fara amfani da kudi domin sayen kuri’ar masu zabe.

A wani jawabi da Jonathan ya raba ga manema labarai yau, Laraba, a Abuja ya ce bai san dalilin da yasa Oshiomhole zai yi kalaman karya a kansa ba. Tsohon shugaban kasar ya ce Oshiomhole na yin barin zance ne saboda matsalolin da suka dabaibaye ofishinsa.

Babbar magana: Jonathan ya saka ayar tambaya a kan lafiyar hankalin Oshiomhole
Jonathan da Oshiomhole
Asali: Depositphotos

Jonathan ya ce an fara sayen kuri’un masu zabe ne a zaben jihar Edo na 2016, shekara daya bayan ya bar ofis.

Ni ina ganin ya rude ne, domin zai yabe ka a yauidan kana APC amma gobe ya kushe ka gobe idan ka fita daga jam’iyyar .

DUBA WANNAN: Sabon salo: PDP ta zo da sabon tsari a zaben fitar da dan takarar shugaban kasa

“Hatta ‘yan jam’iyyarsa bai kyale ba domin ko a yanzu haka akwai matsala tsakaninsa da wasu manyan jami’an gwamnatin APC irin su ministan kwadago, Chris Ngige. Halayensa kadai sun isa su rusa jam’iyyar APC,” a cewar kalaman na Jonathan da mai taimaka masa a bangaren yada labarai, Ikechukwu Eze, ya saka hannu a kai.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng