Hunkuyi ya shiga sahun masu takarar gwamna a jihar Kaduna

Hunkuyi ya shiga sahun masu takarar gwamna a jihar Kaduna

- Sanata mai wakiltan Kaduna ta Arewa a majalisar tarayya, Suleiman Hunkuyi ya sanar da niyarsa na takarar gwamna a jihar Kaduna

- Sanata Hunkuyi zaiyi takaran ne karkashin jam'iyyar PDP

- Hunkuyi ya ce ya shiga takarar ne saboda jama'an Kaduna suna bukatar wani da sauya akalan shugabanci a jihar

Rahoton da muka samu daga Daily Trust na cewa, Sanata Suleiman Uthman Hunkuyi, mai wakiltan Kaduna ta Arewa ya sanar da niyyarsa na tsayawa takarar gwamnan a zaben 2019 karkashin jam'iyyar PDP.

Sanatan da ya sauya sheka daga APC zuwa PDP ya yi wannan sanarwan ne a yau Juma'a a taron jin ra'ayi tare da shugabanin jam'iyyar PDP da masu ruwa da tsaki daga kananan hukumomi 11 a Unguwan Wakili da ke karamar hukumar Zangon Kataf.

Da duminsa: Hunkuyi ya fito takarar gwamna a jihar Kaduna
Da duminsa: Hunkuyi ya fito takarar gwamna a jihar Kaduna
Asali: Facebook

Sanata Hunkuyi ya dade yana sa-in-sa da gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna tun kafin ya baro jam'iyyar APC ya koma PDP.

DUBA WANNAN: An kama wani mutum da ya kira shugaban kasa biri

Wata sanarwa da ta fito daga bakin mai taimakawa sanatan a kafafen yada labarai, ta ce "lokaci ya yi da zamu kawar da wannan canjin a jihar Kaduna."

An sa ran kowanne lokaci daga yanzu, Sanatan zai sayi fam din takarar gwamnan a karkashin jam'iyyar PDP domin shiryawa zaben fitar da gwani a nan gaba.

Sanatan ya ce ya yanke shawarar yin takarar gwamnan ne saboda jama'a suna bukatar wani da zai sauya akalan shugabanci a jihar.

Sanarwan ta kuma ce shugabanin jam'iyyar PDP da masu ruwa da tsaki da suka hallarci taron sunyi alkawarin bawa Hunkuyi goyon baya domin cimma burinsa a jihar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164