2019: APC Sokoto sun tsayar da Shugaba Buhari

2019: APC Sokoto sun tsayar da Shugaba Buhari

Kasa da makonni uku kafin zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress ( APC ), mambobin jam’iyyar babin jihar Sokoto sun tsayar da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a matsayin dan takaran da suke so ya samu tikitin jam’iyyar.

Haka zalika, jam’iyyar ta nuna amincewarta ga shugaban kungiyar sanatocin arewa, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko sannan sun bayyana shi a matsayin shugaba guda a jihar.

Wannan hukunci na daga cikin matsayar da suka tsaya kai a karshen taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da aka gudanar a Sokoto a ranar Talata, 5 ga watan Satumba wadda ya samu halartan shugabannin jam’iyyar a jihar, da masu ruwa da tsaki jam’iyyar.

2019: APC Sokoto sun tsayar da Shugaba Buhari
2019: APC Sokoto sun tsayar da Shugaba Buhari
Asali: Depositphotos

Mataimakin gwamnan jihar, Alhaji Ahmed Aliyu Sokoto ne ya jagoranci ganawar wadda aka gudanar cikin sirri, inda ya bayyana Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko a matsayin uban jam’iyya nagari aa jihar.

KU KARANTA KUMA: Rashin tabbass a Kano yayinda tsohon gwamna Shekarau ya dakatar da sauya shekarsa zuwa APC

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanya ranar zaben fidda gwani na shugaban kasa domin zabar dan takaranta a zaben shugaban kasa na 2019.

Kwamitin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sunce zaben fidda gwani na jam’iyyar mai mulki zai gudana a ranar Alhamis, 20 ga watan Satumba.

Jam’iyyar a tsarin gudanarwan ta tace za’a samar da dan takarar shugaban kasa ta hanyar zaben fidda gwani wato “direct” kenan a turance.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng