Nayi nadamar gaza yiwa PDP wani muhimmin aiki a 2003 – Atiku

Nayi nadamar gaza yiwa PDP wani muhimmin aiki a 2003 – Atiku

A jiya, Litinin, ne Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewar yayi nadamar rashin taimakon jam’iyyar PDP wajen lashe zabuka a jihar Legas a shekarar 2003.

Mai neman PDP ta tsayar da shi takarar shugaban kasa a zaben 2019, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana wa ‘yan jam’iyyar a jihar Legas babbar nadamar sa.

Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito Atiku na fadawa ‘yan majiyar PDP, yayin ganawa dasu a jihar Legas, cewar ya yi nadamar gazawarsa wajen taimakon jam’iyyar ta kafa gwamnati a jihar Legas a shekarar 2003.

Atiku ya yi waiwayen baya a kan yadda tsohon shugaban kasa Obasanjo ya dora masa alhakin tabbatar da jam’iyyar PDP tayi nasara a zabukan shekarar 2003 a jihohin yankin kudu maso yamma da jam’iyyar AD keda karfi a wancan lokacin.

Nayi nadamar gaza yiwa PDP wani muhimmin aiki a 2003 – Atiku
Atiku Abubakar
Asali: Depositphotos

Tsohon shugaban kasar ya ce a lokacin sai da ya yi nasar kawowa jam’iyyar PDP dukkan jihohin yankin kudu maso yamma in banda jihar Legas.

A cewar Atiku, ya kyale jihar Legas ne saboda kyakykyawar dangantaka dake tsakaninsa da tsohon gwamnan jihar Legas a wancan lokacin, Bola Tinubu.

Bayan na nemi Obasanjo ya damka min ragamar yakin neman zabe a jihohin kudu maso yamma kuma ya amince da hakan, nayi nasara a dukkan jihohin yankin in ban da jiharv Legas.

DUBA WANNAN: Jan aiki: PDP ta kafa kwamitin kwace mulki daga hannun APC a karkashin Saraki

“Na kyale Legas ne a wancan lokacin saboda alakar dake tsakanina da tsohon gwamnan jihar, Bola Tinubu, a wancan lokacin.

“Na kyalewa Tinubu Legas ne saboda yadda muka yi gwagwarmayar siyasa tare a SDP da PDM. Amma duk da haka nayi nadamar rashin karbe Legas a wancan lokacin,” a cewar Atiku.

Kazalika, Atiku, ya nemi afuwar ‘yan jam’iyyar ta PDP tare da shaida masu cewar tuni ya yi nadamar barin jihar Legasb da ya yi a hannun Tinubu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng