Na yafewa duk wadanda suka gana min azaba ta tsawon shekara 15 – Al-Mustapha

Na yafewa duk wadanda suka gana min azaba ta tsawon shekara 15 – Al-Mustapha

Manjo Hamza Al-Mustapha, tsohon dogarin tsohon shugabn kasar Najeriya a mulkin soji, marigay Janar Sani Abacha, ya bayyana cewar ya yafewa dukkan masu hannu cikin ukubar da aka shafe shekara 15 ana gana masa.

An kama tare da tsare Al-Mustapha ne bisa zarginsa da kisan Kudirat Abiola, uwargidan mutumin da ya lashe zaben shugaban kasa na shekarar 1993, marigayi Moshood Abiola.

Na yafewa duk wadanda suka gana min azaba ta tsawon shekara 15 – Al-Mustapha
Na yafewa duk wadanda suka gana min azaba ta tsawon shekara 15 – Al-Mustapha

Da yake jawabi a wani taro na kungiyoyin Kiristoci fiye da 40, Al-Mustapha, ya bayyana cewar ya yafewa kafatanin masu hannu a daurin da aka yi masa.

DUBA WANNAN: Mata biyar da suka fi shahara a duniya

A cewar Al-Mustapha, sau 11 ana yunkurin hallaka shi a kan laifin da bai san komai a kai ba amma Allah yana kubutar da shi.

Sannan ya kara da cewar akwai wasu muhimman bayanai da ya samu a kan kungiyar Boko Haram lokacin da yake gidan yari tare da bayyana cewar wasu ‘yan boko ne suka kirkiri kungiyar.

“Sun kawo ‘yan Boko Haram 138 dakin da nake a gidan yari, bayanan da suka sanar da ni ba zan iya fadawa ‘yan Najeriya ba saboda dalilan tsaro” a cewar Al-Mustapha.

Kazalika ya bayyana cewar an kirkiri rikicin makiyaya da manoma dagan-gan domin kawar da hankalin ‘yan Najeriya daga wasu abubuwa dake faruwa a kasa. Sai dai bai bayyana ko wadanne abubuwa ne ba.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel